< Afisawa 4 >

1 A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
Så förmanar jag nu eder, jag fången i Herranom, att I vandren såsom tillbörligit är, i den kallelse, der I uti kallade ären;
2 Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
Med alla ödmjukhet och saktmodighet; med tålamod, unddragandes den ene den andra i kärlekenom;
3 Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
Vinnläggande eder att hålla Andans enhet genom fridsens band;
4 Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
En kropp, och en Ande, såsom I ock kallade ären uti ett edars kallelses hopp;
5 Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
En Herre, en tro, ett dop, en Gud, och allas våra Fader;
6 Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
Hvilken är öfver eder alla, genom eder alla, och i eder alla.
7 Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
Men hvarjom och enom af oss är gifven nåd, efter Christi gåfvos mått.
8 Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
Derföre säger han: Han är uppstigen i höjden, och hafver fört fängelset fånget, och hafver gifvit menniskomen gåfvor.
9 (Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
Men det han uppfaren är, hvad är det annat än han for först härned, uti de nedersta jordenes rum?
10 Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
Den der nederfor, han är ock den der uppfor öfver alla himlar, på det han skulle all ting uppfylla.
11 Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
Han hafver ock somliga satt till Apostlar, somliga till Propheter, somliga till Evangelister, somliga till herdar och lärare;
12 Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
Att de helige skola skickelige vara till ämbetsens verk, genom hvilket Christi lekamen må uppbyggd varda:
13 Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
Tilldess att vi alle kommom till ena tro, och Guds Sons kunskap, och vardom en fullkommen man, den der är uti Christi fullbordiga ålders mått;
14 An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
På det vi icke mer skolom vara barn, och låta oss beveka och omföras af allahanda lärdomsväder, genom menniskors skalkhet och illfundighet, med hvilka de falla till, att de måga bedraga oss.
15 Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
Men varom rättsinnige i kärlekenom, och växom till i all stycke i honom, som hufvudet är, Christus;
16 dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
Af hvilkom hele kroppen tillhopafogas, och en lem hänger intill den andra genom all ledamöten, der den ene tjenar dem andra, efter det verk som hvar lem hafver i sitt mått, och gör att kroppen växer sig sjelf till förbättring, genom kärleken.
17 To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
Så säger jag nu, och betygar det i Herranom, att I icke mer vandren såsom de andre Hedningar vandra, i deras sinnes fåfängelighet;
18 Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
Hvilkas förstånd förmörkradt är, och de bortkomne ifrå det lif som af Gudi är, genom den fåvitsko som i dem är, och genom deras hjertas blindhet;
19 Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
Hvilke, sedan de vordo förstockade, gåfvo de sig sjelfva uti otukt, till att bedrifva all orenlighet, samt med girighet.
20 Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
Men I hafven icke så lärt Christum;
21 Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
Om I annars honom hört hafven, och uti honom lärde ären, huru ett rättsinnigt väsende är i Jesu.
22 sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
Så lägger nu bort ifrån eder den gamla menniskan, der I förra med umgingen, hvilken genom lustar i villfarelse sig förderfvar;
23 A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
Och förnyer eder i edar sinnes anda;
24 Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
Och ikläder eder den nya menniskona, den efter Gud skapad är, i sannskyldiga rättfärdighet och helighet.
25 Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
Derföre, lägger bort lögnen, och taler sanningen, hvar och en med sin nästa; efter vi ärom inbördes lemmar.
26 “Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
Vredgens och synder icke; låter icke solena gå ned öfver edra vrede.
27 kada kuma ku ba wa Iblis dama.
Gifver ock icke lastarenom rum.
28 Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
Den der stulit hafver, han stjäle icke mer; utan heldre arbete med sina händer det godt är; på det han något skall hafva dela med den som nödtorftig är.
29 Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
Intet ohöfviskt tal gånge utaf edar mun; utan det nyttigt är till förbättring, der det behöfves; att det må dem, som det höra, till tacka vara.
30 Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
Och bedröfver icke Guds Helga Anda, der I med beseglade ären till förlossningenes dag.
31 Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
All bitterhet och grymhet, och vrede, och rop, och hädelse vare långt ifrån eder, samt med alla ondsko.
32 Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.
Men varer inbördes till hvarannan vänlige, godhjertige; och förlåter den ene dem andra, såsom ock Gud genom Christum hafver förlåtit eder.

< Afisawa 4 >