< Afisawa 4 >

1 A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
I, then, the prisoner for the Master's sake, entreat you to live and act as becomes those who have received the call that you have received--
2 Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
with all lowliness of mind and unselfishness, and with patience, bearing with one another lovingly, and earnestly striving to maintain,
3 Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
in the uniting bond of peace, the unity given by the Spirit.
4 Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
There is but one body and but one Spirit, as also when you were called you had one and the same hope held out to you.
5 Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
There is but one Lord, one faith, one baptism,
6 Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
and one God and Father of all, who rules over all, acts through all, and dwells in all.
7 Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
Yet to each of us individually grace was given, measured out with the munificence of Christ.
8 Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
For this reason Scripture says: "He re-ascended on high, He led captive a host of captives, and gave gifts to men."
9 (Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
(Now this "re-ascended" --what does it mean but that He had first descended into the lower regions of the earth?
10 Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
He who descended is the same as He who ascended again far above all the Heavens in order to fill the universe.)
11 Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
And He Himself appointed some to be Apostles, some to be Prophets, some to be evangelists, some to be pastors and teachers,
12 Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
in order fully to equip His people for the work of serving--for the building up of Christ's body--
13 Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
till we all of us arrive at oneness in faith and in the knowledge of the Son of God, and at mature manhood and the stature of full-grown men in Christ.
14 An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
So we shall no longer be babes nor shall we resemble mariners tossed on the waves and carried about with every changing wind of doctrine according to men's cleverness and unscrupulous cunning, making use of every shifting device to mislead.
15 Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
But we shall lovingly hold to the truth, and shall in all respects grow up into union with Him who is our Head, even Christ.
16 dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
Dependent on Him, the whole body--its various parts closely fitting and firmly adhering to one another-- grows by the aid of every contributory link, with power proportioned to the need of each individual part, so as to build itself up in a spirit of love.
17 To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
Therefore I warn you, and I implore you in the name of the Master, no longer to live as the Gentiles in their perverseness live,
18 Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
with darkened understandings, having by reason of the ignorance which is deep-seated in them and the insensibility of their moral nature, no share in the Life which God gives.
19 Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
Such men being past feeling have abandoned themselves to impurity, greedily indulging in every kind of profligacy.
20 Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
But these are not the lessons which you have learned from Christ;
21 Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
if at least you have heard His voice and in Him have been taught--and this is true Christian teaching--
22 sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
to put away, in regard to your former mode of life, your original evil nature which is doomed to perish as befits its misleading impulses,
23 A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
and to get yourselves renewed in the temper of your minds and clothe yourselves
24 Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
with that new and better self which has been created to resemble God in the righteousness and holiness which come from the truth.
25 Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
For this reason, laying aside falsehood, every one of you should speak the truth to his fellow man; for we are, as it were, parts of one another.
26 “Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
If angry, beware of sinning. Let not your irritation last until the sun goes down;
27 kada kuma ku ba wa Iblis dama.
and do not leave room for the Devil.
28 Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
He who has been a thief must steal no more, but, instead of that, should work with his own hands in honest industry, so that he may have something of which he can give the needy a share.
29 Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
Let no unwholesome words ever pass your lips, but let all your words be good for benefiting others according to the need of the moment, so that they may be a means of blessing to the hearers.
30 Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
And beware of grieving the Holy Spirit of God, in whom you have been sealed in preparation for the day of Redemption.
31 Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
Let all bitterness and all passionate feeling, all anger and loud insulting language, be unknown among you--and also every kind of malice.
32 Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.
On the contrary learn to be kind to one another, tender-hearted, forgiving one another, just as God in Christ has also forgiven you.

< Afisawa 4 >