< Afisawa 4 >

1 A matsayina na ɗan kurkuku saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi rayuwar da ta dace da kiran da aka yi muku.
Jeg formaner eder derfor, jeg, der fangne i Herren, til at vandre værdig den Kaldelse, med hvilken I bleve kaldede,
2 Kullum ku kasance masu sauƙinkai da kuma hankali; ku zama masu haƙuri, kuna jimrewa da juna cikin ƙauna.
med al Ydmyghed og Sagtmodighed, med Langmodighed, så I bære over med hverandre i Kærlighed
3 Ku yi ƙoƙari sosai ku kiyaye zaman ɗayan nan da Ruhu ya ba ku, ku yi haka ta wurin zaman lafiya da juna.
og gøre eder Flid for at bevare Åndens Enhed i Fredens Bånd;
4 Dukanku jiki ɗaya ne, kuna kuma da Ruhu guda. An ba ku bege guda sa’ad da aka kira ku.
eet Legeme og een Ånd, ligesom I også bleve kaldede til eet Håb i eders Kaldelse;
5 Ubangiji ɗaya, bangaskiya ɗaya, baftisma kuma ɗaya,
een Herre, een Tro, een Dåb,
6 Allah ɗaya Uban duka, wanda yake a bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma.
een Gud og alles Fader, som er over alle og igennem alle og i alle!
7 Amma ga kowannenmu an ba da alheri bisa ga yadda Kiristi ya rarraba.
Men hver enkelt af os blev Nåden given efter Kristi Gaves Mål.
8 Shi ya sa aka ce, “Sa’ad da ya hau sama, ya bi da kamammu kamar tawagarsa ya kuma ba da baye-baye ga mutane.”
Derfor hedder det: "Da han opfor til det høje, bortførte han Fanger og gav Menneskene Gaver."
9 (Me ake nufin da “ya hau,” in ba cewa dā ya sauka can ƙarƙashin ƙasa ba?
Men dette: "Han opfor," hvad er det, uden at han også nedfor til Jordens nedre Egne.
10 Shi wannan da ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau zuwa can sama, kai, gaba da sammai, don mulkinsa yă cika duniya gaba ɗaya.)
Han, som nedfor, han er også den, som opfor højt over alle. Himlene, for at han skulde fylde alle Ting.
11 Saboda haka Kiristi kansa ya ba wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu su zama annabawa, waɗansu su zama masu wa’azi, waɗansu kuma su zama fastoci, da kuma malamai.
Og han gav nogle som Apostle, andre som Profeter, andre som Evangelister, andre som Hyrder og Lærere,
12 Ya yi haka don yă shirya mutanensa saboda ayyukan hidima, don a gina jikin Kiristi.
til de helliges fuldkomne Beredelse, til en Tjenestegerning, til Kristi Legemes Opbyggelse,
13 Wannan zai ci gaba har sai mun zama ɗaya a cikin bangaskiya da kuma ta wurin fahimtarmu na Ɗan Allah. Sa’an nan za mu zama balagaggu, kamar yadda Kiristi yake, mu kuma zama gaba ɗaya cikakku kamar sa.
indtil vi alle nå til Enheden i Troen på og Erkendelsen af Guds Søn, til Mands Modenhed, til Kristi Fyldes Mål af Vækst,
14 An yi wannan kuwa don kada mu koma zama kamar yara, muna ta canja zukatanmu game da abin da muka gaskata don kawai wani ya faɗa mana wani abu dabam, ko domin wani ya yi wayo ya ruɗe mu, ya sa ƙarya ta zama kamar gaskiya.
for at vi ikke; mere skulle være umyndige, der omtumles og omdrives af enhver Lærdommens Vind, ved Menneskenes Tærningspil, ved Træskhed efter Vildfarelsens Rænkespind;
15 Ya kamata kullum ƙauna tă sa mu faɗa gaskiya. Ta haka za mu yi girma a kowace hanya, mu kuma zama kamar Kiristi, wanda yake kan
men for at vi, Sandheden tro i Kærlighed, skulle i alle Måder opvokse til ham, som er Hovedet, Kristus,
16 dukan jiki. Shi ne ya haɗe jiki duka, ya kuma sa dukan gaɓoɓin jiki suna aiki daidai, yayinda kowace gaɓa take aikinta cikin ƙauna.
ud fra hvem hele Legemet, idet det sammenføjes og sammenknyttes ved ethvert hjælpende Bindeled i Forhold til hver enkelt Dels tilmålte Virkekraft, fuldbyrder Legemets Vækst til Opbyggelse af sig selv i Kærlighed.
17 To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
Dette siger jeg da og vidner i Herren, at I skulle ikke mere vandre, således som Hedningerne vandre i deres Sinds Tomhed,
18 Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
formørkede i deres Tanke, fremmedgjorte for Guds Liv som Følge af den Vankundighed, som er i dem på Grund af deres Hjertes Forhærdelse,
19 Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
de, som jo følesløse have hengivet sig til Uterligheden, til at øve al Urenhed i Havesyge.
20 Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
Men I have ikke således lært Kristus,
21 Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
om I da have hørt om ham og ere blevne oplærte i ham, således som Sandhed er i Jesus,
22 sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
at I, hvad eders forrige Vandel angår, skulle aflægge det gamle Menneske, som fordærves ved bedrageriske Begæringer,
23 A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
men fornyes i eders Sinds Ånd
24 Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
og iføre eder det nye Menneske, som blev skabt efter Gud i Sandhedens Retfærdighed og Hellighed.
25 Saboda haka dole kowannenku yă bar yin ƙarya, yă kuma riƙa faɗa wa maƙwabcinsa gaskiya, gama dukanmu gaɓoɓi jiki ɗaya ne.
Derfor aflægger Løgnen og taler Sandhed, hver med sin Næste, efterdi vi ere hverandres Lemmer.
26 “Cikin fushinku kada ku yi zunubi.” Kada ku bar rana ta fāɗi kuna fushi,
Blive I vrede, da synder ikke; lad ikke Solen gå ned over eders Forbitrelse;
27 kada kuma ku ba wa Iblis dama.
giver ikke heller Djævelen Rum!
28 Duk wanda yake sata, sai yă daina sata, dole kuma yă yi aiki, yă yi wani abu mai amfani da hannuwansa, don yă sami abin da zai iya raba da masu bukata.
Den, som stjæler, stjæle ikke mere, men arbejde hellere og gøre det gode med sine egne Hænder, for at han kan have noget at meddele den, som er i Trang.
29 Kada wata ƙazamar magana ta fita daga bakunanku, sai dai abin da yake da amfani don gina waɗansu bisa ga bukatunsu. Ta haka maganarku za tă zama da amfani ga masu jinta.
Lad ingen rådden Tale udgå af eders Mund, men sådan Tale, som er god til fornøden Opbyggelse, for at den kan skaffe dem Nåde, som høre derpå;
30 Kada kuma ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda da shi aka hatimce ku da shi don ranar fansa.
og bedrøver ikke Guds hellige Ånd, med hvilken I bleve beseglede til Forløsningens Dag.
31 Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, haushi da hasala, faɗa da ɓata suna, ku rabu da kowace irin ƙeta.
Al Bitterhed og Hidsighed og Vrede og Skrigen og Forhånelse blive langt fra eder tillige med al Ondskab!
32 Ku yi alheri, ku kuma ji tausayin juna, kuna gafarta wa juna, kamar yadda a cikin Kiristi, Allah ya gafarta muku.
Men vorder velvillige imod hverandre, barmhjertige, tilgivende hverandre, ligesom jo Gud har tilgivet eder i Kristus.

< Afisawa 4 >