< Afisawa 2 >

1 Ku kam, a dā ku matattu ne saboda laifofinku da kuma zunubanku.
E vos vivificou, estando vós mortos pelas offensas e peccados,
2 Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. (aiōn g165)
Em que d'antes andastes segundo o curso d'este mundo, segundo o principe da potestade do ar, do espirito que agora opera nos filhos da desobediencia. (aiōn g165)
3 Dukanmu a dā mun yi irin rayuwan nan a cikinsu, muna bin kwaɗayi da sha’awace-sha’awacen jikunanmu da tunaninmu. Kamar sauran mutane, mun cancanci fushin Allah.
Entre os quaes todos nós tambem d'antes andavamos nos desejos da nossa carne, fazendo a vontade da carne e dos pensamentos; e eramos por natureza filhos da ira, como os outros tambem.
4 Amma saboda yawan ƙaunar da yake mana, Allah, wanda yake mai yawan jinƙai,
Porque Deus, que é riquissimo em misericordia, pelo seu muito amor com que nos amou,
5 ya ba mu rai sa’ad da ya tashe Kiristi daga matattu. Ta wurin alherin Allah ne aka cece ku.
Estando nós ainda mortos em nossas offensas, nos vivificou juntamente com Christo (pela graça sois salvos),
6 Allah ya tashe mu tare da Kiristi, ya kuma ba mu wurin zama tare da shi a cikin mulkin samaniya.
E nos resuscitou juntamente, e nos fez assentar juntamente nos céus, em Christo Jesus;
7 Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. (aiōn g165)
Para mostrar nos seculos vindouros as abundantes riquezas da sua graça, pela sua benignidade para comnosco em Christo Jesus. (aiōn g165)
8 Allah ya cece ku ta wurin alheri sa’ad da kuka ba da gaskiya. Wannan kuwa ba yinku ba ne, kyauta ce daga Allah.
Porque pela graça sois salvos, por meio da fé; e isto não vem de vós; é dom de Deus
9 Ba kuwa saboda aikin lada ba, don kada wani yă ɗaga kai.
Não vem das obras, para que ninguem se glorie.
10 Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Kiristi Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.
Porque somos feitura sua, creados em Christo Jesus para as boas obras, as quaes Deus preparou para que andassemos n'ellas.
11 Saboda haka, ku tuna dā ku Al’ummai ne bisa ga haihuwa, waɗanda kuma ake kira masu “kaciya” sukan kira ku “marasa kaciya” (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu).
Portanto, lembrae-vos de que vós d'antes ereis gentios na carne, e chamados incircumcisão pelos que na carne se chamam circumcisão feita pela mão dos homens;
12 Ku kuma tuna a lokacin ba ku san Kiristi ba. A ware kuke daga mutanen Isra’ila, ba ku kuma da dangantaka da alkawaran da Allah ya yi da su. Kun yi zama a duniyan nan babu bege kuma babu Allah.
Que n'aquelle tempo estaveis sem Christo, separados da communidade d'Israel, e estranhos aos concertos da promessa, não tendo esperança, e sem Deus no mundo.
13 Amma yanzu a cikin Kiristi Yesu, ku da dā kuke can da nesa an kawo ku kusa ta wurin jinin Kiristi.
Mas agora em Christo Jesus, vós, que d'antes estaveis longe, já pelo sangue de Christo chegastes perto.
14 Gama shi kansa shi ne salamarmu, shi ne ya kawo ƙungiyoyi biyu suka zama ɗaya, ya kuma rushe katangan nan ta ƙiyayya wadda ta raba mu.
Porque elle é a nossa paz, o qual de ambos os povos fez um; e, derribando a parede de separação que estava no meio,
15 Kiristi ya ba da jikinsa don yă kawar da doka da dukan umarnanta da kuma ƙa’idodinta. Ya yi haka domin yă halicci sabuwar zuriya daga zuriyoyin nan biyu. Ta haka kuma ya kawo salama tsakaninsu.
Na sua carne desfez a inimizade, a saber, a lei dos mandamentos, que consistia em tradições, para crear em si mesmo os dois em um novo homem, fazendo a paz,
16 A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah.
E pela cruz reconciliar com Deus a ambos em um corpo, matando n'ella as inimizades.
17 Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa.
E, vindo, elle evangelizou a paz, a vós que estaveis longe, e aos que estavam perto;
18 Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.
Porque por elle ambos temos accesso em um mesmo Espirito ao Pae.
19 Don haka, yanzu ku ba baƙi ba ne, ku kuma ba bare ba ne. Ku’yan ƙasa ne tare da mutanen Allah, iyalin gidan Allah kuma.
Assim que já não sois estrangeiros, nem forasteiros, mas concidadãos dos sanctos e domesticos de Deus;
20 Ku gini ne wanda manzanni da annabawa suke tushensa, Kiristi kuma shi ne dutse mafi muhimmanci na ginin.
Edificados sobre o fundamento dos apostolos e dos prophetas, de que Jesus Christo é a principal pedra da esquina;
21 Ta wurinsa ne dukan ginin yake a haɗe, shi ne kuma yake sa ginin yă yi girma, yă zama haikali mai tsarki domin Ubangiji.
No qual todo o edificio, bem ajustado, cresce para templo sancto no Senhor.
22 Ku ma sashe ne na wannan ginin da Kiristi ya yi inda Allah yake zaune ta wurin Ruhunsa.
No qual tambem vós juntamente sois edificados para morada de Deus em Espirito.

< Afisawa 2 >