< Afisawa 2 >

1 Ku kam, a dā ku matattu ne saboda laifofinku da kuma zunubanku.
He[F] raised you up as well, when you were dead in your transgressions and sins,
2 Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. (aiōn g165)
in which you once walked, according to the Aeon of this world, the ruler of the domain of the air, the spirit who is now at work in the sons of the disobedience; (aiōn g165)
3 Dukanmu a dā mun yi irin rayuwan nan a cikinsu, muna bin kwaɗayi da sha’awace-sha’awacen jikunanmu da tunaninmu. Kamar sauran mutane, mun cancanci fushin Allah.
among whom all of us also used to conduct ourselves in the lusts of our flesh, carrying out the desires of the flesh and of the senses, and were by nature children of wrath, just like the rest.
4 Amma saboda yawan ƙaunar da yake mana, Allah, wanda yake mai yawan jinƙai,
But God—being rich in mercy, because of His great love with which He loved us,
5 ya ba mu rai sa’ad da ya tashe Kiristi daga matattu. Ta wurin alherin Allah ne aka cece ku.
even when we were dead in our transgressions—made us alive together with Christ (by grace you have been saved)
6 Allah ya tashe mu tare da Kiristi, ya kuma ba mu wurin zama tare da shi a cikin mulkin samaniya.
and raised us up together and seated us together in the heavenly realms in Christ Jesus,
7 Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. (aiōn g165)
in order that in the coming ages He might display the surpassing riches of His grace, through His kindness toward us in Christ Jesus. (aiōn g165)
8 Allah ya cece ku ta wurin alheri sa’ad da kuka ba da gaskiya. Wannan kuwa ba yinku ba ne, kyauta ce daga Allah.
For by grace you have been saved, through the Faith—and this not of yourselves, it is the gift of God—
9 Ba kuwa saboda aikin lada ba, don kada wani yă ɗaga kai.
not by works, so that no one may boast.
10 Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Kiristi Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.
You see, we are His ‘poem’, created in Christ Jesus for good works, which God prepared in advance in order that we should walk in them.
11 Saboda haka, ku tuna dā ku Al’ummai ne bisa ga haihuwa, waɗanda kuma ake kira masu “kaciya” sukan kira ku “marasa kaciya” (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu).
So then, remember that once you physical Gentiles—called ‘uncircumcision’ by the so-called ‘circumcision’ (that made in flesh with hands)—
12 Ku kuma tuna a lokacin ba ku san Kiristi ba. A ware kuke daga mutanen Isra’ila, ba ku kuma da dangantaka da alkawaran da Allah ya yi da su. Kun yi zama a duniyan nan babu bege kuma babu Allah.
that at that time you were apart from Christ, excluded from citizenship in Israel and strangers to the covenants of the promise, having no hope and without God in the world.
13 Amma yanzu a cikin Kiristi Yesu, ku da dā kuke can da nesa an kawo ku kusa ta wurin jinin Kiristi.
But now in Christ Jesus you who once were far away have come to be near through the blood of the Christ.
14 Gama shi kansa shi ne salamarmu, shi ne ya kawo ƙungiyoyi biyu suka zama ɗaya, ya kuma rushe katangan nan ta ƙiyayya wadda ta raba mu.
For He Himself is our peace, who has made both one and broken down the barrier of separation—the law with its commandments and ordinances—
15 Kiristi ya ba da jikinsa don yă kawar da doka da dukan umarnanta da kuma ƙa’idodinta. Ya yi haka domin yă halicci sabuwar zuriya daga zuriyoyin nan biyu. Ta haka kuma ya kawo salama tsakaninsu.
having abolished the enmity through His ‘flesh’, so as to mold the two [Jew and Gentile] into one new man in Himself (thus making peace),
16 A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah.
and to reconcile them both in one body to God through the cross (by which He killed the enmity).
17 Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa.
He came and proclaimed peace to us, being both far and near,
18 Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.
because through Him we both have access to the Father, by one Spirit.
19 Don haka, yanzu ku ba baƙi ba ne, ku kuma ba bare ba ne. Ku’yan ƙasa ne tare da mutanen Allah, iyalin gidan Allah kuma.
So then, you are no longer strangers and aliens, but fellow citizens with the saints and members of God's household,
20 Ku gini ne wanda manzanni da annabawa suke tushensa, Kiristi kuma shi ne dutse mafi muhimmanci na ginin.
built upon the foundation of the apostles and prophets, Jesus Christ Himself being the chief cornerstone;
21 Ta wurinsa ne dukan ginin yake a haɗe, shi ne kuma yake sa ginin yă yi girma, yă zama haikali mai tsarki domin Ubangiji.
in whom the whole building, being joined together, grows into a holy temple in the Lord;
22 Ku ma sashe ne na wannan ginin da Kiristi ya yi inda Allah yake zaune ta wurin Ruhunsa.
in whom you also are being built together to become a habitation of God in spirit.

< Afisawa 2 >