< Afisawa 1 >
1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
Paul, an Apostle of Christ Jesus by the will of God: To God's people who are in Ephesus--believers in Christ Jesus.
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
May grace and peace be granted to you from God our Father and the Lord Jesus Christ.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, who has crowned us with every spiritual blessing in the heavenly realms in Christ;
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
even as, in His love, He chose us as His own in Christ before the creation of the world, that we might be holy and without blemish in His presence.
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
For He pre-destined us to be adopted by Himself as sons through Jesus Christ--such being His gracious will and pleasure--
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
to the praise of the splendour of His grace with which He has enriched us in the beloved One.
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
It is in Him, and through the shedding of His blood, that we have our deliverance--the forgiveness of our offences--so abundant was God's grace,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
the grace which He, the possessor of all wisdom and understanding, lavished upon us,
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
when He made known to us the secret of His will. And this is in harmony with God's merciful purpose
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
for the government of the world when the times are ripe for it--the purpose which He has cherished in His own mind of restoring the whole creation to find its one Head in Christ; yes, things in Heaven and things on earth, to find their one Head in Him.
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
In Him we Jews have been made heirs, having been chosen beforehand in accordance with the intention of Him whose might carries out in everything the design of His own will,
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
so that we should be devoted to the extolling of His glorious attributes--we who were the first to fix our hopes on Christ.
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
And in Him you Gentiles also, after listening to the Message of the truth, the Good News of your salvation--having believed in Him--were sealed with the promised Holy Spirit;
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
that Spirit being a pledge and foretaste of our inheritance, in anticipation of its full redemption--the inheritance which He has purchased to be specially His for the extolling of His glory.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
For this reason I too, having heard of the faith in the Lord Jesus which prevails among you, and of your love for all God's people,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
offer never ceasing thanks on your behalf while I make mention of you in my prayers.
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
For I always beseech the God of our Lord Jesus Christ--the Father most glorious--to give you a spirit of wisdom and penetration through an intimate knowledge of Him,
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
the eyes of your understanding being enlightened so that you may know what is the hope which His call to you inspires, what the wealth of the glory of His inheritance in God's people,
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
and what the transcendent greatness of His power in us believers as seen in the working of His infinite might
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
when He displayed it in Christ by raising Him from the dead and seating Him at His own right hand in the heavenly realms,
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn )
high above all other government and authority and power and dominion, and every title of sovereignty used either in this Age or in the Age to come. (aiōn )
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
God has put all things under His feet, and has appointed Him universal and supreme Head of the Church, which is His Body,
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
the completeness of Him who everywhere fills the universe with Himself.