< Afisawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
I, Paul, am an apostle whom God appointed (to represent/to proclaim the message about) Christ Jesus because that is what God wanted. [I am writing this letter] to you who are the people of God in Ephesus [city. You are people who] (faithfully/continue to) trust in Christ Jesus and who have a close relationship with him.
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
[I pray that] God our Father and Jesus Christ our Lord will continue to act kindly toward you and cause you to have [inner] peace.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Praise God, the Father of our Lord Jesus Christ! Because of our relationship with Christ, he has blessed us spiritually in every way by giving us blessings that come from heaven.
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
Before God created the world, he chose us to be his people because of our (relationship with/union with) Christ, in order that [God could consider] us to be completely holy [DOU]. Because [God] loves [us],
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
he decided long ago that he would adopt us to be [as though we were] his own children because of what Jesus Christ [has done]. He decided to do that because it pleased him to do that.
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
He did it in order that we would praise him for acting very kindly toward us in a wonderful way that we did not deserve. He did it because of our relationship with his beloved Son {[one, who is also God, whom he] loves}.
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
When the blood of Christ [flowed when he died] [MTY], [it was as though] he paid a price to free/save us [from the guilt of our sins]. [That] ([provided a way/made it possible]) [for] God to act very kindly toward us to forgive us for having sinned.
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
He acted very kindly toward us and enabled us to become wise about many [HYP] things and to understand his truth.
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
He has enabled us to know the things that he had planned secretly (OR, that he had not revealed to anyone yet). He did that because he wanted to do that, and because he planned to do that by means of the things Christ would do.
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
God planned that at the time that [he appointed], he would unite all things/beings in heaven and all things/beings on earth (OR, all beings in heaven and all things on earth), and cause Christ to be the one who will rule them [MET].
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
Because of our close relationship with Christ, God has also chosen us [(inc)] (OR, us [(exc)] Jews) to receive what he has promised [to give] us. He decided long ago to do that. It was exactly what he planned. He accomplishes everything exactly as he plans and desires,
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
in order that we(exc) Jews, who confidently expected the Messiah to do great things for us before the non-Jews expected such things (OR, we [(inc)] who were already confidently expecting Christ [to do great things for us]) will praise him for his greatness.
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
You [Ephesians] also heard the true message, the good message about how God saves you. [People] put their seal on something to show that [it belongs to them]. Similarly, when you believed [in Christ], God [showed that you also belong to him by sending you] the Holy Spirit as he promised to do [MET].
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
The Holy Spirit is [like] [MET] a (deposit/down payment). That is, he (guarantees/assures us) that [we will receive] all that God has promised to give us, at the time when God will give to those who belong to him [MET] everything that [Christ] freed us to receive. [God also assures you that you belong to him], in order that you would praise him for his greatness.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
Because of [what God has done for you], and because [people] told me that you continue to trust in the Lord Jesus and that you love all those who belong to God,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
I thank God for you constantly [LIT, HYP]. I (mention/pray for) you constantly, whenever I pray.
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
[I pray] that God, who is the glorious/wonderful Father of our Lord Jesus Christ, may cause his Spirit to make you wise, and that his Spirit will reveal [God to you] so that you may fully know him.
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
And I pray that God would enable you to understand [MTY] his truth, in order that in your (inner beings/hearts) you may know the things that we believers should confidently expect to receive because he chose us [to be his people]. And I pray that you will know how God will bless his people in a very wonderful way [when we finally receive] all that he has promised to give us.
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
And [I pray that] you will know how very powerfully [God helps] us who continue to trust [in Christ]. He works powerfully for us
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
just like he acted powerfully for Christ when he caused Christ to become alive again after he died, and put him in the place of highest/greatest honor [MTY] in heaven.
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
[There], Christ is the supreme ruler over every powerful spirit of every level of authority. His rank is much higher than any powerful spirit can receive, not only now, but forever. (aiōn g165)
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
God has caused all beings to be subject to Christ [MTY], and he has also appointed Christ, who rules over all things, to rule [MET] over all believers.
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
We believers [relate to Christ like the parts of a person’s] body [MET] [relate to its head]. Christ uses all [his power among us] just like he uses his power throughout the whole universe.

< Afisawa 1 >