< Afisawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
Paul, an apostle of Christ Jesus by the will of God, to the saints who are [[in Ephesus]], and believers in Christ Jesus:
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace be to you, and peace, from God our Father, and the Lord Jesus Christ.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Blessed be God, the Father of our Lord Jesus Christ, who blessed us with every spiritual blessing in the heavenly regions in Christ;
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
according as he chose us in him, before the foundation of the world, that we should be holy and blameless before him;
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
having in love predestinated us for himself to be adopted as sons through Jesus Christ, according to the good pleasure of his will,
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
to the praise of the glory of his grace, which he freely bestowed on us in the Beloved;
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
in whom we have the redemption through his blood, the forgiveness of our trespasses, according to the riches of his grace,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
which he made to abound toward us, in all wisdom and understanding;
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
having made known to us the mystery of his will, according to his good pleasure which he purposed in himself
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
in reference to the dispensation of the fullness of the times, to gather for himself into one all things in Christ, the things which are in the heavens, and the things on the earth; even in him,
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
in whom we also obtained the inheritance, being predestinated according to the purpose of him who worketh all things after the counsel of his own will,
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
that we should be to the praise of his glory, we who have before placed our hope in the Messiah;
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
in whom ye also, after having heard the word of truth, the glad tidings of your salvation, in whom, I say, having also believed, ye were sealed with the Holy Spirit that was promised,
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
which is a pledge of our inheritance until the redemption of the purchased possession, to the praise of his glory.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
For this cause I also, having heard of your faith in the Lord Jesus, and of your love to all the saints,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
do not cease to give thanks for you, making mention of you in my prayers;
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
that the God of our Lord Jesus Christ, the Father of glory, would give to you the spirit of wisdom and revelation in the full knowledge of him;
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
the eyes of your mind being enlightened, that ye may know what is the hope belonging to his call of you, and what the riches of the glory of the inheritance which he hath given among the saints,
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
and what the exceeding greatness of his power toward us who believe, according to the working of his mighty power,
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
which he wrought in Christ, when he raised him from the dead; and seated him at his own right hand in the heavenly regions,
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
far above all rule, and authority, and power, and dominion, and every name that is named, not only in this world, but also in that which is to come; (aiōn g165)
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
and put all things in subjection under his feet, and gave him to be head over all things to the church,
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
which is his body, the fullness of him who filleth all with all;

< Afisawa 1 >