< Mai Hadishi 9 >

1 Sai na yi tunani a kan wannan na kuma gane cewa masu adalci da masu hikima da kuma abubuwan da suke yi suna a hannun Allah ne, amma ba wanda ya san ko ƙauna ko ƙiyayya ce take jiransa.
For I gave my mind to all this, even to search out all this, that the righteous and the wise and their works are in the hand of God, and yet neither his love nor hatred doth any man know. All is before them.
2 Dukansu makomarsu ɗaya ce, masu adalci da masu mugunta, masu kirki da marasa kirki, masu tsabta da marasa tsabta, masu miƙa hadaya da waɗanda ba sa yi. Kamar yadda yake ga mutumin kirki, haka yake ga mai zunubi. Kamar yadda yake ga masu yin rantsuwa, haka ma da masu tsoron yi.
All [[cometh to them]] as to all. There is one event to the righteous and to the wicked; to the good, to the clean, and to the unclean; to him that sacrificeth, and to him that sacrificeth not; as is the good, so is the sinner; he that sweareth, as he that feareth an oath.
3 Wannan ita ce muguntar da take faruwa a cikin dukan abubuwa a duniya. Ƙaddara ɗaya ce take a kan kowa. Amma zukatan mutane cike suke da mugunta, akwai kuma hauka a zukatansu yayinda suke a raye, bayan haka kuma sai su mutu.
This is an evil among all things which take place under the sun, that there is one event to all; therefore also the heart of the sons of men is full of evil, and madness is in their heart while they live, and afterward they go down to the dead.
4 Duk wanda yake da rai a wannan duniya ta rayayyu, yana sa zuciya, gara rayayyen kare da mataccen zaki!
For who is there that is excepted? With all the living there is hope; for a living dog is better than a dead lion.
5 Gama rayayyu sun san za su mutu, amma matattu ba su san kome ba; ba su da wata lada nan gaba an manta da su ke nan gaba ɗaya.
For the living know that they shall die; but the dead know not any thing, and there is no more to them any advantage, for their memory is forgotten.
6 Ƙaunarsu, ƙiyayyarsu, da kuma kishinsu tuni sun ɓace; ba za su taɓa zama sashen wani abin da yake faruwa a duniya ba.
Their love also, and their hatred, and their envy, is now perished; neither have they a portion any more for ever in any thing which taketh place under the sun.
7 Yi tafiyarka, ka ci abincinka da farin ciki, ka sha ruwan inabinka da farin zuciya, gama abin da ka yi duka daidai ne a wurin Allah.
Go thy way, eat thy bread with joy, and drink thy wine with a cheerful heart; for long since hath God been pleased with thy works.
8 Kullum ka kasance cikin farin riguna, ka kuma shafe kanka da mai kullum,
Let thy garments be always white, and let not fragrant oil be wanting upon thy head.
9 Ka more rayuwa da matarka, wadda kake ƙauna, dukan kwanakin nan marasa amfani da Allah ya ba ka a duniya. Gama wannan ne rabonka a rayuwa da kuma na faman aikinka a duniya.
Enjoy life with the wife whom thou lovest, all the days of thy vain life which he hath given thee under the sun, all thy vain days. For this is thy portion in life, and in thy labor with which thou weariest thyself under the sun.
10 Duk abin da hannunka yake yi, ka yi shi da dukan ƙarfinka, gama a cikin kabari in da za ka, babu aiki ko shirye-shirye, ko sani, ko hikima. (Sheol h7585)
Whatever thy hand findeth to do, do it with thy might! For there is no work nor device nor knowledge nor wisdom in the under-world, whither thou goest. (Sheol h7585)
11 Na kuma ga wani abu a duniya. Ba kullum maguji ne yake nasara a tsere ba, ba kullum jarumi ne yake yin nasara ba, ba kullum mai hikima ne da abinci ba ba kullum mai basira ne yake da wadata ba ba kullum gwani ne yake samun tagomashi ba; amma sa’a, da tsautsayi, sukan sami kowannensu.
I turned and saw under the sun, that the race is not to the swift, nor the battle to the strong, nor yet bread to the wise, nor riches to men of understanding, nor favor to men of knowledge; but time and chance happen to them all.
12 Ban da haka ma, ba wanda ya san sa’ad da lokacin mutuwarsa zai yi. Kamar yadda akan kama kifi a muguwar raga, ko a kama tsuntsu a tarko, haka mugun lokaci yakan auko wa mutane, ba tsammani.
For man knoweth not his time. As fishes that are taken in a destructive net, and as birds that are caught in a snare, so are the sons of men snared in a time of distress, when it falleth suddenly upon them.
13 Na kuma ga wani misali game da hikima a duniya wanda ya burge ni sosai.
This also have I seen; even wisdom under the sun, and it seemed great to me.
14 An yi wani ɗan ƙaramin birni mai mutane kaɗan a ciki. Sai wani babban sarki ya kawo masa yaƙi, ya kafa masa babban sansani.
There was a little city, and few men within it; and a great king came against it, and besieged it, and built great bulwarks against it.
15 A cikin birnin nan kuwa akwai wani mutum matalauci amma mai hikima, ya kuma ceci birnin ta wurin hikimarsa. Amma ba wanda ya tuna da matalaucin nan.
Now there was found within it a wise poor man; and he, by his wisdom, delivered the city; yet no man remembered that same poor man.
16 Sai na ce, “Hikima ta fi ƙarfe ƙarfi.” Amma aka rena hikimar matalaucin, ba a ma jin maganarsa.
Then said I, “Wisdom is better than strength;” and yet the poor man's wisdom is despised, and his words are not heard.
17 Raɗar mai hikima da aka saurara cikin natsuwa ta fi ihun mai mulkin wawaye.
The quiet words of the wise are sooner heard than the shouting of a foolish ruler.
18 Hikima ta fi kayan yaƙi, amma mai zunubi ɗaya yakan rushe alheri mai yawa.
Wisdom is better than weapons of war. But one offender destroyeth much good.

< Mai Hadishi 9 >