< Mai Hadishi 8 >
1 Wa yake kama da mai hikima? Wa ya san bayanin abubuwa? Hikima takan haskaka fuskar mutum, ta kuma kawo sakin fuska.
Hvem er som den vise, og hvem forstår å tyde tingene? Visdommen gjør menneskets ansikt lyst, og trossen i hans åsyn forvandles.
2 Ka yi biyayya da umarnin sarki, na ce, saboda alkawarin da ka yi a gaban Allah.
Jeg sier: Akt på kongens bud, og det for den eds skyld som du har svoret ved Gud!
3 Kada ka yi hanzarin tashi daga gaban sarki. Kada ka kāre abin da ba daidai ba, gama zai iya yin duk abin da ya ga dama.
Vær ikke for snar til å forlate ham, og vær ikke med på noget som er ondt! For han gjør alt det han vil.
4 Da yake maganar sarki ita ce mafificiya, wa zai iya ce masa, “Me kake yi?”
For kongens ord er mektig, og hvem tør si til ham: Hvad gjør du?
5 Duk wanda ya yi biyayya da umarninsa ba zai sami lahani ba, zuciya mai hikima kuma zai san lokacin da ya dace da kuma hanyoyin da suka fi.
Den som holder budet, skal ikke lide noget ondt, og den vises hjerte skal få kjenne tid og dom.
6 Gama akwai lokaci da hanyoyin da suka dace da yin kowane abu, ko da yake wahalar mutum ta yi masa yawa.
For hvert foretagende har sin tid og sin dom; for hvert menneskes onde gjerning kommer til å hvile tungt på ham;
7 Da yake ba wanda ya san nan gaba, wa zai iya faɗa masa abin da zai faru?
for han vet ikke hvad som skal hende; for hvem kan si ham hvorledes det vil gå?
8 Ba wanda yake da iko a kan iska har da zai riƙe ta, saboda haka babu mai iko kan ranar mutuwarsa. Kamar yadda ba a sallamar mutum a lokacin yaƙi, haka ma mugunta ba za tă saki masu aikata ta ba.
Intet menneske har makt over vinden, så han kan holde den tilbake; heller ikke har nogen makt over dødsdagen, og ingen slipper for å gjøre krigstjeneste. Således kan heller ikke ugudelighet berge sin mann.
9 Na ga dukan waɗannan, yayinda na lura da kowane abin da ake yi a duniya. Akwai lokacin da mutum yakan nauyaya wa waɗansu ba da sonsa ba.
Alt dette har jeg sett, og jeg har gitt akt på alt det som hender under solen, på en tid da det ene menneske hersket over det andre og voldte ham ulykke.
10 Sa’an nan kuma, na ga an binne masu mugunta, waɗanda suke shiga da fita daga tsattsarkan wuri suke kuma samun yabo a birnin da suka yi wannan. Wannan ma ba shi da amfani.
Derefter så jeg at ugudelige blev jordfestet og kom til hvile, men at de som hadde gjort rett, måtte dra bort fra den Helliges bolig og blev glemt i staden. Også dette er tomhet.
11 In ba a hanzarta aka yanke hukunci a kan laifi ba, zukatan mutane sukan cika da ƙulle-ƙullen aikata abubuwan da ba daidai ba.
Fordi dommen over den onde gjerning ikke fullbyrdes straks, derfor svulmer hjertet i menneskenes barn, så de drister sig til å gjøre det som ondt er,
12 Ko da yake mugu ya aikata laifi ɗari ya kuma yi tsawon rai, na san cewa zai fi wa masu tsoron Allah kyau, waɗanda suke girmama Allah.
fordi synderen hundre ganger gjør det som ondt er, og allikevel lever lenge; dog vet jeg jo at det skal gå gudfryktige vel, fordi de frykter Gud,
13 Duk da haka, domin masu mugunta ba su ji tsoron Allah ba, abubuwa ba za su yi musu kyau ba, ransu kamar inuwa yake ba zai yi tsawo ba.
men at det ikke skal gå den ugudelige vel, og at han lik skyggen ikke skal leve lenge, fordi han ikke frykter Gud.
14 Akwai kuma wani abu marar amfani da yake faruwa a duniya, masu adalci sukan sha hukuncin da ya dace da masu mugunta, masu mugunta kuma sukan karɓi sakayyar da ya cancanci masu adalci su samu. Na ce, wannan ma, ba shi da amfani.
Der er noget tomt som hender på jorden: at der er rettferdige hvem det går som om de hadde gjort de ugudeliges gjerninger, og at der er ugudelige hvem det går som om de hadde gjort de rettferdiges gjerninger. Jeg sier at også dette er tomhet.
15 Saboda haka abin da na ce, shi ne mutum yă ji daɗi, domin iyakar jin daɗinsa a wannan rai, shi ne yă ci, yă sha, yă ji wa kansa daɗi. Aƙalla yana iya yin wannan in ya yi aiki a kwanakin da Allah ya ba shi a wannan duniya.
Så priste jeg da gleden, fordi mennesket ikke har noget annet godt under solen enn å ete og drikke og være glad; og dette følger ham under hans strev i de levedager som Gud har gitt ham under solen.
16 Da na mai da hankalina don in sami hikima in kuma lura da wahalar mutum a duniya, ko da a ce idanunsa ba sa barci dare da rana,
Da jeg vendte min hu til å lære visdom å kjenne og til å se på det strev og kav folk har her på jorden - for hverken dag eller natt får de søvn på sine øine -
17 sam, ba zai taɓa fahimci abin da Allah yake yi ba. Iyakar ƙoƙarin da ka yi duk ba za ka iya ganewa ba. Masu hikima suna iya cewa sun sani, amma kuwa ba su sani ba.
da så jeg at det er så med alt Guds verk at mennesket ikke kan utgrunde det som hender under solen; for hvor meget et menneske enn strever med å utgranske det, kan han dog ikke utgrunde det, og selv om den vise sier at han nok skal forstå det, er han dog ikke i stand til å utgrunde det.