< Mai Hadishi 8 >

1 Wa yake kama da mai hikima? Wa ya san bayanin abubuwa? Hikima takan haskaka fuskar mutum, ta kuma kawo sakin fuska.
Qui connaît les raisons véritables? Qui sait la solution des choses? La sagesse de l'homme se reflète sur son visage; le front de l'impudent inspire la haine.
2 Ka yi biyayya da umarnin sarki, na ce, saboda alkawarin da ka yi a gaban Allah.
Observe le commandement du roi, et cela, à cause de la parole que Dieu a jurée.
3 Kada ka yi hanzarin tashi daga gaban sarki. Kada ka kāre abin da ba daidai ba, gama zai iya yin duk abin da ya ga dama.
Ne te hâte pas de t'éloigner de Sa face; ne tiens pas à la parole si elle est coupable: car il fera tout ce Qu'il voudra;
4 Da yake maganar sarki ita ce mafificiya, wa zai iya ce masa, “Me kake yi?”
comme fait un roi puissant; et qui pourra lui dire: Qu'as-tu fait?
5 Duk wanda ya yi biyayya da umarninsa ba zai sami lahani ba, zuciya mai hikima kuma zai san lokacin da ya dace da kuma hanyoyin da suka fi.
Celui qui observe les commandements ne connaîtra pas le mal, le cœur du sage sait le temps du jugement de Dieu.
6 Gama akwai lokaci da hanyoyin da suka dace da yin kowane abu, ko da yake wahalar mutum ta yi masa yawa.
Car pour toutes choses il y a temps et jugement, et l'homme en sait beaucoup sur lui-même.
7 Da yake ba wanda ya san nan gaba, wa zai iya faɗa masa abin da zai faru?
Mais nul ne sait ce qui doit arriver: que sera-ce? Qui le lui fera connaître?
8 Ba wanda yake da iko a kan iska har da zai riƙe ta, saboda haka babu mai iko kan ranar mutuwarsa. Kamar yadda ba a sallamar mutum a lokacin yaƙi, haka ma mugunta ba za tă saki masu aikata ta ba.
Il n'est point d'homme qui ait pouvoir sur la vie, qui puisse la retenir; il n'a pas plus de pouvoir sur le jour de la mort; et il n'est point pour lui de trêve au jour de la bataille, et l'impiété ne sauvera pas ceux qui l'aiment.
9 Na ga dukan waɗannan, yayinda na lura da kowane abin da ake yi a duniya. Akwai lokacin da mutum yakan nauyaya wa waɗansu ba da sonsa ba.
Et j'ai vu toutes ces choses, et j'ai appliqué mon cœur à toute œuvre qui se fait sous le soleil; et j'ai vu les choses où l'homme a pris pouvoir sur l'homme, pour l'affliger.
10 Sa’an nan kuma, na ga an binne masu mugunta, waɗanda suke shiga da fita daga tsattsarkan wuri suke kuma samun yabo a birnin da suka yi wannan. Wannan ma ba shi da amfani.
Et j'ai vu des impies conduits à la sépulture, au sortir du lieu saint, et ils étaient allés dans leur voie, et ils avaient été loués dans la ville, parce qu'ils avaient ainsi fait; et cela encore est vanité.
11 In ba a hanzarta aka yanke hukunci a kan laifi ba, zukatan mutane sukan cika da ƙulle-ƙullen aikata abubuwan da ba daidai ba.
Car, parce que ceux qui font le mal ne sont point repris incontinent, le cœur des fils des hommes s'enhardit par leur exemple à mal faire.
12 Ko da yake mugu ya aikata laifi ɗari ya kuma yi tsawon rai, na san cewa zai fi wa masu tsoron Allah kyau, waɗanda suke girmama Allah.
Celui qui une fois a péché, a fait le mal depuis lors, et longtemps. Et moi je sais que Dieu est bon pour ceux qui craignent en Sa présence.
13 Duk da haka, domin masu mugunta ba su ji tsoron Allah ba, abubuwa ba za su yi musu kyau ba, ransu kamar inuwa yake ba zai yi tsawo ba.
Mais le bonheur ne sera pas pour l'impie, et il n'aura pas de longs jours; ils passeront comme l'ombre, parce qu'il ne craint pas la face de Dieu.
14 Akwai kuma wani abu marar amfani da yake faruwa a duniya, masu adalci sukan sha hukuncin da ya dace da masu mugunta, masu mugunta kuma sukan karɓi sakayyar da ya cancanci masu adalci su samu. Na ce, wannan ma, ba shi da amfani.
Voici encore une vanité qui existe sur la terre: il est des justes à qui il arrive comme à l'œuvre des impies; il est des impies à qui il arrive comme à l'œuvre des justes. Et cela, ai-je dit, est encore vanité.
15 Saboda haka abin da na ce, shi ne mutum yă ji daɗi, domin iyakar jin daɗinsa a wannan rai, shi ne yă ci, yă sha, yă ji wa kansa daɗi. Aƙalla yana iya yin wannan in ya yi aiki a kwanakin da Allah ya ba shi a wannan duniya.
Et c'est pourquoi (dit l'impie) j'ai loué toutes les joies; car il n'est rien de meilleur pour l'homme sous le soleil, sinon de manger, de boire et de se réjouir. Et cela seul lui restera de tout le labeur qu'il fait durant les jours de la vie que Dieu lui a données sous le soleil.
16 Da na mai da hankalina don in sami hikima in kuma lura da wahalar mutum a duniya, ko da a ce idanunsa ba sa barci dare da rana,
Dans ces pensées, j'ai appliqué mon cœur à connaître la sagesse, et à voir l'inquiétude qui naît sur la terre; car la nuit comme le jour, il n'est personne qui de ses yeux voie le sommeil.
17 sam, ba zai taɓa fahimci abin da Allah yake yi ba. Iyakar ƙoƙarin da ka yi duk ba za ka iya ganewa ba. Masu hikima suna iya cewa sun sani, amma kuwa ba su sani ba.
Et j'ai vu toutes les œuvres de Dieu, et j'ai vu que l'homme ne pourra jamais s'expliquer l'œuvre qui se fait sous le soleil. Quelque fatigue qu'il se donne pour chercher, il ne la trouvera pas et, quelque science même que le sage croie avoir, il ne pourra la trouver.

< Mai Hadishi 8 >