< Mai Hadishi 5 >
1 Ka lura da matakanka sa’ad da ka tafi gidan Allah. Ka je kusa don ka saurara a maimakon miƙa hadaya kamar wawaye, waɗanda ba su san sun yi laifi ba.
Пильнуй за ногою своєю, як до Божого дому йдеш, бо прийти, щоб послухати, — це краще за жертву безглуздих, бо не знають нічо́го вони, окрім чи́нення зла!
2 Kada ka yi subul da bakinka, kada zuciyarka tă yi garajen furta wani abu a gaban Allah. Allah yana sama kai kuma kana duniya, saboda haka, kada kalmominka su zama da yawa.
Не квапся своїми уста́ми, і серце твоє нехай не поспішає казати слова́ перед Божим лицем, — Бог бо на небі, а ти на землі, тому́ то нехай нечисле́нними будуть слова́ твої!
3 Kamar yadda son cika buri yakan zo sa’ad da kana da yawan damuwa, haka jawabin wawa yake sa’ad da yake yawan magana.
Бо як сон наступає через велику роботу, так багато слів має і голос безглу́здого.
4 Sa’ad da ka yi alkawari ga Allah, kada ka ɓata lokaci wajen cika shi. Ba ya jin daɗin wawaye; ka cika alkawarinka.
Коли зробиш обі́тницю Богові, то не зволікай її виповнити, бо в Нього нема уподо́бання до нерозумних, а що́ ти обі́туєш, спо́вни!
5 Gara kada ka yi alkawari, da ka yi amma ba ka cika ba.
Краще не дати обі́ту, ніж дати обіт — і не спо́внити!
6 Kada ka bar bakinka ya kai ga yin zunubi. Kada kuma ka kai ƙara wurin ɗan saƙon haikali cewa, “Alkawarin da na yi kuskure ne.” Me ya sa Allah yake fushi a kan abin da ka faɗa har yă lalatar da aikin hannuwanka?
Не давай своїм у́стам впроваджувати своє тіло у гріх, і не говори перед Анголом Божим: „Це помилка!“Пощо Бог буде гні́ватися на твій голос, і діла́ твоїх рук буде нищити?
7 Yawan buri da yawan magana ba su da amfani. Saboda haka, ka ji tsoron Allah.
Бо марно́та в числе́нності снів, як і в мно́гості слів, але ти бійся Бога!
8 In ka ga ana zaluntar matalauta a wani yanki, ba a yin adalci, ana kuma tauye hakki, kada ka yi mamakin waɗannan abubuwa; domin akwai wani jami’in da yake bisa da wani, a bisansu biyu kuwa akwai wani.
Якщо ти побачиш у кра́ї якому ути́скування бідаря́ та пору́шення права та правди, не дивуйся тій речі, бо високий пильнує згори́ над високим, а над ними Всевишній.
9 Kowa yakan amfana da bunkasar amfanin ƙasa, sarki kansa yana samun riba daga gonaki.
І пожи́ток землі є для всіх, бо поле й сам цар обробляє.
10 Duk mai ƙaunar kuɗi ba ya samun isashe; duk ma ƙaunar dukiya ba ya ƙoshi da abin da yake samu. Wannan ma ba shi da amfani.
Хто срі́бло кохає, той не наси́титься сріблом, хто ж кохає багатство з прибу́тком, це марно́та також!
11 Kamar yadda kaya suke haɓaka, haka ma masu amfani da su. Kuma wane amfani ne suke ga mai shi in ba ciyar da idanunsa a kansu ba?
Як маєток примно́жується, то мно́жаться й ті, що його поїдають, і яка ко́ристь його власникові, як тільки, щоб бачили очі його?
12 Barcin ma’aikaci daɗi gare shi, ko yă ci kaɗan ko da yawa, amma yalwar mai arziki ba ta barinsa yă iya yin barci.
Сон солодкий в трудя́щого, чи багато, чи мало він їсть, а ситість багатого спати йому не дає.
13 Na ga wani mugun abu a duniya, arzikin da aka ajiye don yă cuce mai shi,
Є лихо болюче, я бачив під сонцем його: багатство, яке береже́ться його власнико́ві на лихо йому, —
14 ko kuwa dukiyar da ta ɓace ta wata hasara, har ya zama sa’ad da ya haifi ɗa, babu abin da ya bar masa.
і гине багатство таке в нещасли́вім випа́дку, а ро́диться син — і немає нічого у нього в руці:
15 Tsirara mutum yakan fito daga cikin mahaifiyarsa, kuma kamar yadda ya fito, haka zai koma. Ba ya ɗaukan kome daga wahalarsa da zai riƙe a hannunsa.
як він вийшов наги́й із утро́би матері своєї, так відхо́дить ізнов, як прийшов, і нічо́го не винесе він з свого тру́ду, що можна б узяти своєю рукою!
16 Wannan ma mugun abu ne, Yadda mutum ya zo, haka zai koma, to, wace riba ce ya ci, da yake ya yi wahalar iska ce kawai?
І це те́ж зло болюче: так само, як він був прийшов, так віді́йде, — і яка йому ко́ристь, що трудився на вітер?
17 Duk rayuwarsa ya ci abinci a cikin duhu, da ɓacin rai mai tsanani, da azaba, da fushi.
А до того всі дні свої їв у темно́ті, і багато мав смутку, й хвороби та люті.
18 Sa’an nan na gane cewa abu mai kyau ne, daidai ne kuma mutum yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗin aikin da ya yi a’yan kwanakin da Allah ya ba shi, gama wannan shi aka ƙaddara wa mutum daga faman wahalarsa a duniya a cikin’yan kwanakin da Allah ya ba shi a duniya, gama wannan shi ne rabonsa.
Оце, що я бачив, як добре та гарне: щоб їла люди́на й пила, і щоб бачила добре в усьо́му своє́му труді́, що під сонцем ним тру́диться в час нечисле́нних тих днів свого віку, які Бог їй дав, — бо це доля її!
19 Ban da haka ma, sa’ad da Allah ya ba wa mutum dukiya da wadata, ya kuma ba shi zarafi yă ji daɗinsu, ya kuma amince da rabonsa, sai yă ji daɗin aikinsa, wannan kyauta ce ta Allah.
Також кожна люди́на, що Бог дав їй багатство й маєтки, і вла́ду їй дав спожива́ти із то́го, та брати свою частку та тішитися своїм тру́дом, — то це Божий дару́нок!
20 Da ƙyar yake tunani a kan kwanakin rayuwarsa, domin Allah ya yarje masa, yă zauna da farin ciki.
Бо вона днів свого життя небагато на пам'яті матиме, — то Бог в її серце шле радість!