< Mai Hadishi 5 >
1 Ka lura da matakanka sa’ad da ka tafi gidan Allah. Ka je kusa don ka saurara a maimakon miƙa hadaya kamar wawaye, waɗanda ba su san sun yi laifi ba.
Bevara din fot, när du går till Guds hus, och kom till att höra; det är bättre, än de dårars offer; ty de veta icke hvad ondt de göra.
2 Kada ka yi subul da bakinka, kada zuciyarka tă yi garajen furta wani abu a gaban Allah. Allah yana sama kai kuma kana duniya, saboda haka, kada kalmominka su zama da yawa.
Var icke för hastig med dinom mun, och låt ditt hjerta icke hasta till att något tala inför Gud; ty Gud är i himmelen, och du på jordene; derföre låt din ord vara få.
3 Kamar yadda son cika buri yakan zo sa’ad da kana da yawan damuwa, haka jawabin wawa yake sa’ad da yake yawan magana.
Ty der många omsorger äro, der komma drömmer, och der mång ord äro, der hörer man en dåra.
4 Sa’ad da ka yi alkawari ga Allah, kada ka ɓata lokaci wajen cika shi. Ba ya jin daɗin wawaye; ka cika alkawarinka.
När du gör Gudi ett löfte, så fördröj icke fullkomnat; ty han hafver intet behag till dårar. Hvad du lofvar, det håll.
5 Gara kada ka yi alkawari, da ka yi amma ba ka cika ba.
Det är bättre att du intet lofvar, än att du icke håller det du lofvar.
6 Kada ka bar bakinka ya kai ga yin zunubi. Kada kuma ka kai ƙara wurin ɗan saƙon haikali cewa, “Alkawarin da na yi kuskure ne.” Me ya sa Allah yake fushi a kan abin da ka faɗa har yă lalatar da aikin hannuwanka?
Städ icke dinom mun, att han förförer ditt kött, och säg icke för Ängelen: Jag är oskyldig. Gud måtte vredgas öfver dina röst, och fördöma all dina händers verk.
7 Yawan buri da yawan magana ba su da amfani. Saboda haka, ka ji tsoron Allah.
Der månge drömmer äro, der är fåfängelighet, och många ord; men frukta du Gud.
8 In ka ga ana zaluntar matalauta a wani yanki, ba a yin adalci, ana kuma tauye hakki, kada ka yi mamakin waɗannan abubuwa; domin akwai wani jami’in da yake bisa da wani, a bisansu biyu kuwa akwai wani.
Ser du enom fattigom ske orätt, och rätt och rättviso i landena borttagas, förundra dig icke deröfver; ty det är ännu en högre väktare öfver de höga, och äro ännu högre öfver de båda.
9 Kowa yakan amfana da bunkasar amfanin ƙasa, sarki kansa yana samun riba daga gonaki.
Deröfver är Konungen i hela landet, att marken må varda brukad.
10 Duk mai ƙaunar kuɗi ba ya samun isashe; duk ma ƙaunar dukiya ba ya ƙoshi da abin da yake samu. Wannan ma ba shi da amfani.
Den som älskar penningen, han varder aldrig mätt af penningar, och den der rikedom kär hafver, han skall ingen nytto få deraf; det är ock fåfängelighet.
11 Kamar yadda kaya suke haɓaka, haka ma masu amfani da su. Kuma wane amfani ne suke ga mai shi in ba ciyar da idanunsa a kansu ba?
Ty der mycket gods är, der äro månge som ätat; och hvad nytto hafver han deraf, som det hafver, annat än att han ser deruppå med ögonen?
12 Barcin ma’aikaci daɗi gare shi, ko yă ci kaɗan ko da yawa, amma yalwar mai arziki ba ta barinsa yă iya yin barci.
Den der arbetar, honom är sömnen söt, ehvad han hafver litet eller mycket ätit; men dens rikas öfverflödighet städer honom icke sofva.
13 Na ga wani mugun abu a duniya, arzikin da aka ajiye don yă cuce mai shi,
Det är en ond plåga, som jag såg under solene, nämliga att rikedomar varda förvarade honom till skada, som dem äger.
14 ko kuwa dukiyar da ta ɓace ta wata hasara, har ya zama sa’ad da ya haifi ɗa, babu abin da ya bar masa.
Ty den rike förgås med stor jämmer; och om han hafver födt en son, honom blifver intet i händerna.
15 Tsirara mutum yakan fito daga cikin mahaifiyarsa, kuma kamar yadda ya fito, haka zai koma. Ba ya ɗaukan kome daga wahalarsa da zai riƙe a hannunsa.
Såsom han är naken kommen af sitt moderlif, så far han bort igen, som han kommen är, och tager intet med sig af allt sitt arbete i sine hand, när han bortfar.
16 Wannan ma mugun abu ne, Yadda mutum ya zo, haka zai koma, to, wace riba ce ya ci, da yake ya yi wahalar iska ce kawai?
Det är en ond plåga, att han så hädanfar, som han kommen är; hvad hjelper det honom då, att han i vädret arbetat hafver?
17 Duk rayuwarsa ya ci abinci a cikin duhu, da ɓacin rai mai tsanani, da azaba, da fushi.
Alla sina lifsdagar hafver han ätit i mörkret, och i stor grämelse, och krankhet, och bedröfvelse.
18 Sa’an nan na gane cewa abu mai kyau ne, daidai ne kuma mutum yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗin aikin da ya yi a’yan kwanakin da Allah ya ba shi, gama wannan shi aka ƙaddara wa mutum daga faman wahalarsa a duniya a cikin’yan kwanakin da Allah ya ba shi a duniya, gama wannan shi ne rabonsa.
Så håller jag det nu for det bästa, när man äter och dricker, och är vid ett godt mod, i allt arbete, som en gör under solene alla sina lifsdagar, som Gud honom gifver; ty det är hans del.
19 Ban da haka ma, sa’ad da Allah ya ba wa mutum dukiya da wadata, ya kuma ba shi zarafi yă ji daɗinsu, ya kuma amince da rabonsa, sai yă ji daɗin aikinsa, wannan kyauta ce ta Allah.
Ty hvilko mennisko Gud gifver rikedom, och ägodelar, och välde, att hon deraf äter och dricker på sin del, och är glad i sitt arbete, det är en Guds gåfva.
20 Da ƙyar yake tunani a kan kwanakin rayuwarsa, domin Allah ya yarje masa, yă zauna da farin ciki.
Ty han tänker icke mycket på detta elända lifvet, efter Gud fröjdar hans hjerta.