< Mai Hadishi 5 >

1 Ka lura da matakanka sa’ad da ka tafi gidan Allah. Ka je kusa don ka saurara a maimakon miƙa hadaya kamar wawaye, waɗanda ba su san sun yi laifi ba.
Put your feet down with care when you go to the house of God, for it is better to give ear than to make the burned offerings of the foolish, whose knowledge is only of doing evil.
2 Kada ka yi subul da bakinka, kada zuciyarka tă yi garajen furta wani abu a gaban Allah. Allah yana sama kai kuma kana duniya, saboda haka, kada kalmominka su zama da yawa.
Be not unwise with your mouth, and let not your heart be quick to say anything before God, because God is in heaven and you are on the earth — so let not the number of your words be great.
3 Kamar yadda son cika buri yakan zo sa’ad da kana da yawan damuwa, haka jawabin wawa yake sa’ad da yake yawan magana.
As a dream comes from much business, so the voice of a foolish man comes with words in great number.
4 Sa’ad da ka yi alkawari ga Allah, kada ka ɓata lokaci wajen cika shi. Ba ya jin daɗin wawaye; ka cika alkawarinka.
When you take an oath before God, put it quickly into effect, because he has no pleasure in the foolish; keep the oath you have taken.
5 Gara kada ka yi alkawari, da ka yi amma ba ka cika ba.
It is better not to take an oath than to take an oath and not keep it.
6 Kada ka bar bakinka ya kai ga yin zunubi. Kada kuma ka kai ƙara wurin ɗan saƙon haikali cewa, “Alkawarin da na yi kuskure ne.” Me ya sa Allah yake fushi a kan abin da ka faɗa har yă lalatar da aikin hannuwanka?
Let not your mouth make your flesh do evil. And say not before the angel, It was an error. So that God may not be angry with your words and put an end to the work of your hands.
7 Yawan buri da yawan magana ba su da amfani. Saboda haka, ka ji tsoron Allah.
Because much talk comes from dreams and things of no purpose. But let the fear of God be in you.
8 In ka ga ana zaluntar matalauta a wani yanki, ba a yin adalci, ana kuma tauye hakki, kada ka yi mamakin waɗannan abubuwa; domin akwai wani jami’in da yake bisa da wani, a bisansu biyu kuwa akwai wani.
If you see the poor under a cruel yoke, and law and right being violently overturned in a country, be not surprised, because one authority is keeping watch on another and there are higher than they.
9 Kowa yakan amfana da bunkasar amfanin ƙasa, sarki kansa yana samun riba daga gonaki.
It is good generally for a country where the land is worked to have a king.
10 Duk mai ƙaunar kuɗi ba ya samun isashe; duk ma ƙaunar dukiya ba ya ƙoshi da abin da yake samu. Wannan ma ba shi da amfani.
He who has a love for silver never has enough silver, or he who has love for wealth, enough profit. This again is to no purpose.
11 Kamar yadda kaya suke haɓaka, haka ma masu amfani da su. Kuma wane amfani ne suke ga mai shi in ba ciyar da idanunsa a kansu ba?
When goods are increased, the number of those who take of them is increased; and what profit has the owner but to see them?
12 Barcin ma’aikaci daɗi gare shi, ko yă ci kaɗan ko da yawa, amma yalwar mai arziki ba ta barinsa yă iya yin barci.
The sleep of a working man is sweet, if he has little food or much; but to him who is full, sleep will not come.
13 Na ga wani mugun abu a duniya, arzikin da aka ajiye don yă cuce mai shi,
There is a great evil which I have seen under the sun — wealth kept by the owner to be his downfall.
14 ko kuwa dukiyar da ta ɓace ta wata hasara, har ya zama sa’ad da ya haifi ɗa, babu abin da ya bar masa.
And I saw the destruction of his wealth by an evil chance; and when he became the father of a son he had nothing in his hand.
15 Tsirara mutum yakan fito daga cikin mahaifiyarsa, kuma kamar yadda ya fito, haka zai koma. Ba ya ɗaukan kome daga wahalarsa da zai riƙe a hannunsa.
As he came from his mother at birth, so does he go again; he gets from his work no reward which he may take away in his hand.
16 Wannan ma mugun abu ne, Yadda mutum ya zo, haka zai koma, to, wace riba ce ya ci, da yake ya yi wahalar iska ce kawai?
And this again is a great evil, that in all points as he came so will he go; and what profit has he in working for the wind?
17 Duk rayuwarsa ya ci abinci a cikin duhu, da ɓacin rai mai tsanani, da azaba, da fushi.
All his days are in the dark, and he has much sorrow, pain, disease, and trouble.
18 Sa’an nan na gane cewa abu mai kyau ne, daidai ne kuma mutum yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗin aikin da ya yi a’yan kwanakin da Allah ya ba shi, gama wannan shi aka ƙaddara wa mutum daga faman wahalarsa a duniya a cikin’yan kwanakin da Allah ya ba shi a duniya, gama wannan shi ne rabonsa.
This is what I have seen: it is good and fair for a man to take meat and drink and to have joy in all his work under the sun, all the days of his life which God has given him; that is his reward.
19 Ban da haka ma, sa’ad da Allah ya ba wa mutum dukiya da wadata, ya kuma ba shi zarafi yă ji daɗinsu, ya kuma amince da rabonsa, sai yă ji daɗin aikinsa, wannan kyauta ce ta Allah.
Every man to whom God has given money and wealth and the power to have pleasure in it and to do his part and have joy in his work: this is given by God.
20 Da ƙyar yake tunani a kan kwanakin rayuwarsa, domin Allah ya yarje masa, yă zauna da farin ciki.
He will not give much thought to the days of his life; because God lets him be taken up with the joy of his heart.

< Mai Hadishi 5 >