< Mai Hadishi 3 >

1 Akwai lokaci domin kowane abu, da kuma lokaci domin kowane aiki a duniya.
For everything there is a season, and a time for every purpose under heaven:
2 Lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin shuki da lokacin tumɓukewa.
a time to be born, and a time to die, a time to plant, and a time to pluck up that which is planted,
3 Lokacin kisa da lokacin warkarwa, lokacin rushewa da lokacin ginawa.
a time to kill, and a time to heal, a time to break down, and a time to build up,
4 Lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa.
a time to weep, and a time to laugh, a time to mourn, and a time to dance,
5 Lokacin warwatsa duwatsu da lokacin tara su, lokacin runguma da lokacin dainawa.
a time to cast away stones, and a time to gather stones together, a time to embrace, and a time to refrain from embracing,
6 Lokacin nema, da lokacin fid da zuciya, lokacin ajiyewa da lokacin zubarwa.
a time to seek, and a time to lose, a time to keep, and a time to cast away,
7 Lokacin yagewa da lokacin ɗinkewa, lokacin yin shiru da lokacin magana.
a time to tear, and a time to sew, a time to keep silence, and a time to speak,
8 Lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.
a time to love, and a time to hate, a time for war, and a time for peace.
9 Wace riba ce ma’aikaci yake da ita saboda wahalarsa?
What profit has he who works in that in which he labors?
10 Na ga nawayar da Allah ya ɗora a kan mutane.
I have seen the travail which God has given to the sons of men to be employed therewith.
11 Ya yi kowane abu da kyau a lokacinsa. Ya kuma sa matuƙa a zukatan mutane, duk da haka sun kāsa gane abin da Allah ya yi daga farko zuwa ƙarshe.
He has made everything beautiful in its time. Also he has set eternity in their heart, yet so that man cannot find out the work that God has done from the beginning even to the end.
12 Na san ba abin da ya fi wa mutane kyau fiye da su ji daɗi su kuma yi alheri yayinda suke da rai.
I know that there is nothing better for them, than to rejoice, and to do good as long as they live.
13 Cewa kowa yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗi cikin dukan aikinsa, wannan kyautar Allah ce.
And also that every man should eat and drink, and enjoy good in all his labor. It is the gift of God.
14 Na san cewa duk abin da Allah ya yi zai dawwama har abada; ba abin da za a ƙara ko a rage. Allah ya yi haka domin mutane su girmama shi.
I know that, whatever God does, it shall be forever. Nothing can be put to it, nor anything taken from it. And God has done it that men should fear before him.
15 Duk abin da yana nan ya taɓa kasancewa, kuma abin da zai kasance, ya taɓa kasancewa; Allah kuma zai nemi bayanin abubuwan da suka wuce.
That which is, has been long ago, and that which is to be, has long ago been. And God seeks again that which has passed away.
16 Sai na ga wani abu kuma a duniya, a wurin shari’a, akwai mugunta a can, a wurin adalci, akwai mugunta a can.
And moreover I saw under the sun, in the place of justice, that wickedness was there, and in the place of righteousness, that wickedness was there.
17 Sai na yi tunani a zuciyata, “Allah zai shari’anta masu adalci da masu mugunta, gama za a kasance da lokaci domin kowane aiki, lokaci domin kowane abu.”
I said in my heart, God will judge the righteous man and the wicked man, for there is a time there for every purpose and for every work.
18 Na sāke yin tunani, “Game da mutane kam, Allah kan gwada su don su san cewa ba su fi dabba ba.
I said in my heart, It is because of the sons of men, that God may prove them, and that they may see that they themselves are beasts.
19 Ƙaddarar mutum ɗaya take da ta dabba; ƙaddara ɗaya ce take jiransu biyu. Yadda ɗayan yake mutuwa, haka ma ɗayan. Dukansu numfashinsu iri ɗaya ne; mutum bai fi dabba ba. Kowane abu ba shi da amfani.
For that which befalls the sons of men befalls beasts, even one thing befalls them; as the one dies, so dies the other. Yea, they all have one breath, and man has no preeminence above the beasts; for all is vanity.
20 Duka wuri ɗaya za su tafi; gama duka daga turɓaya suka fito, kuma ga turɓaya duka za su koma.
All go to one place. All are of the dust, and all turn to dust again.
21 Wa ya tabbatar cewa ruhun mutum yakan tashi sama sa’an nan na dabba yă sauka ƙasa?”
Who knows the spirit of man, whether it goes upward, and the spirit of the beast, whether it goes downward to the earth?
22 Saboda haka na ga babu abin da ya fi kyau wa mutum fiye da yă more wahalar aikinsa, domin wannan ne rabonsa. Gama wa zai kawo shi yă ga abin da zai faru a bayansa?
Therefore I saw that there is nothing better, than that a man should rejoice in his works, for that is his portion. For who shall bring him back to see what shall be after him?

< Mai Hadishi 3 >