< Mai Hadishi 2 >
1 Na ce wa kaina, “Zo, zan gwada ka da jin daɗi don in ga abin da yake da kyau.” Amma wannan ma ya zama ba amfani.
Jeg sagde ved mig selv: »Vel, jeg vil prøve med Glæde; saa nyd da det gode!« Men se, ogsaa det var Tomhed.
2 Sai na ce, “Dariya hauka ce. Kuma me jin daɗi yake kawowa?”
Om Latteren sagde jeg: »Daarskab!« og om Glæden: »Hvad gavner den?«
3 Na yi ƙoƙari in sa raina yă yi farin ciki da ruwan inabi, in kuma rungumi wauta, hankalina kuma yana yin mini jagora da hikima. Na so in ga abin da yake da daraja ga mutane a duniya a’yan kwanakinsu.
Jeg kom paa den Tanke at kvæge mit Legeme med Vin, medens mit Hjerte dog raadede med Visdom, og at slaa mig paa Daarskab, indtil jeg saa, hvad det baader Menneskens Børn at gøre under Himmelen, det Dagetal de lever.
4 Na yi ayyuka masu girma. Na gina gidaje wa kaina na kuma shuka gonakin inabi.
Jeg fuldbyrdede store Værker, byggede mig Huse, plantede mig Vingaarde,
5 Na yi lambuna da wuraren shaƙatawa, na shuka itatuwa masu’ya’ya iri-iri a cikinsu.
anlagde mig Haver og Lunde og plantede alle Haande Frugttræer deri,
6 Na yi tankuna don in yi banruwan kurmin itatuwa.
anlagde mig Damme til at vande en Skov i Opvækst;
7 Na sayi bayi mata da maza, ina kuma da waɗansu bayin da aka haifa a gidana. Ina da garkunan shanu da na tumaki da na awaki fiye da duk wanda ya taɓa zama a Urushalima kafin ni.
jeg købte Trælle og Trælkvinder, og jeg havde hjemmefødte Trælle; ogsaa Kvæg, Hornkvæg og Smaakvæg, havde jeg i større Maader end nogen af dem, der før mig havde været i Jerusalem;
8 Na tara wa kaina azurfa da zinariya, ina da ma’ajin sarakuna da yankuna. Na samo wa kaina mawaƙa mata da maza, da dukan irin matan da kowane namiji zai so.
jeg samlede mig ogsaa Sølv og Guld, Skatte fra Konger og Lande; jeg tog mig Sangere og Sangerinder og Menneskens Børns Lyst: Hustru og Hustruer.
9 Na ƙasaita fiye da kowane mutumin da ya riga ni zama a Urushalima. Cikin dukan wannan, hikimata ba tă rabu da ni ba.
Og jeg blev stor, større end nogen af dem, der før mig havde været i Jerusalem; desuden blev min Visdom hos mig.
10 Ban hana kaina duk wani abin da idona ya yi sha’awarsa ba; ban hana zuciyata wani jin daɗi ba. Zuciyata ta yi murna da dukan aikina, wannan kuwa shi ne ladan dukan famata.
Intet, som mine Øjne attraaede, unddrog jeg dem; jeg nægtede ikke mit Hjerte nogen Glæde thi mit Hjerte havde Glæde af al min Flid, og deri laa Lønnen for al min Flid.
11 Duk da haka sa’ad da na duba dukan aikin hannuwana, da abin da na yi fama don in samu, sai kome ya zama ba shi da amfani, naushin iska ne kawai; babu wata riba a duniya.
Men da jeg overskuede alt, hvad mine Hænder havde virket, og den Flid, det havde kostet mig, se, da var det alt sammen Tomhed og Jag efter Vind, og der er ingen Vinding under Solen.
12 Sai na juya ga tunanina don in lura da hikima, da kuma hauka da wauta. Me ya rage wa magājin sarki yă yi fiye da abin da aka riga aka yi?
Thi hvad gør det Menneske, som kommer efter Kongen? Det samme, som tilforn er gjort? Jeg gav mig da til at sammenligne Visdom med Daarskab og Taabelighed.
13 Na ga cewa hikima ta fi wauta, kamar yadda haske ya fi duhu.
Jeg saa, at Visdom har samme Fortrin for Taabelighed som Lys for Mørke:
14 Mai hikima ya san inda ya nufa, wawa kuwa yana tafiya a cikin duhu; amma sai na gane cewa ƙaddara ɗaya ce take samunsu.
Den vise har Øjne i Hovedet, men Taaben vandrer i Mørke. Men jeg skønnede ogsaa, at en og samme Skæbne rammer begge.
15 Sai na yi tunani a zuciyata, “Ƙaddarar wawa za tă same ni ni ma. Wace riba ce hikimata za tă jawo mini?” Na ce a zuciyata, “Wannan ma ba shi da amfani.”
Da sagde jeg ved mig selv: »Taabens Skæbne rammer ogsaa mig; hvad har jeg da for, at jeg er blevet overvættes viis?« Og jeg sagde ved mig selv, at ogsaa det er Tomhed;
16 Gama ba za a ƙara tunawa da mai hikima ko wawa ba; nan gaba za a manta da su. Yadda wawa zai mutu, haka ma mai hikima!
thi den vises Minde er lige saa lidt evigt som Taabens, fordi nu engang alt glemmes i kommende Dage; ak! den vise maa dø saa godt som Taaben.
17 Don haka na ƙi jinin rayuwa, gama aikin da ake yi a duniya yana ɓata mini rai. Dukan abin da yake cikinta kuwa ba shi da amfani, naushin iska ne kawai.
Da blev jeg led ved Livet, thi ilde tyktes mig det, som sker under Solen; thi det er alt sammen Tomhed og Jag efter Vind.
18 Na ƙi jinin dukan abubuwan da na yi wahala ina yi a duniya, gama dole in bar su wa na bayana.
Og jeg blev led ved al den Flid, jeg, har gjort mig under Solen, fordi jeg maa efterlade mit Værk til den, som kommer efter mig.
19 Wa ya sani ko zai zama mai hikima ko kuma wawa? Duk da haka zai mallaki dukan aikin da na yi da ƙoƙarina da kuma dabarata a duniya. Wannan ma ba shi da amfani.
Hvo ved, om det bliver en Vismand eller en Taabe? Og dog skal han raade over alt, hvad jeg med Flid og Visdom vandt under Solen. Ogsaa det er Tomhed.
20 Saboda haka zuciyata ta fara karaya a kan dukan faman aikina a duniya.
Og jeg var ved at fortvivle over al den Flid, jeg har gjort mig under Solen;
21 Gama mutum zai yi aikinsa da dukan hikimarsa, da saninsa, da gwanintarsa, sa’an nan dole yă bar dukan abin da ya mallaka ga wani wanda bai yi wahalar kome a ciki ba. Wannan ma ba shi da amfani, hasara ce mai yawa.
thi der har et Menneske gjort sig. Flid med Visdom, Kundskab og Dygtighed, og saa maa han overlade sit Eje til et Menneske, som ikke har lagt Flid derpaa. Ogsaa det er Tomhed og et stort Onde.
22 Me mutum zai samu daga aikin da ya yi duka, da irin ɗawainiyar da ya sha a kan yin aikin a duniya?
Thi hvad faar et Menneske for al sin Flid og sit Hjertes Higen, som han gør sig Flid med under Solen?
23 Dukan kwanakinsa aikinsa damuwa ce da ɓacin zuciya; ko da dare ma hankalinsa ba a kwance yake ba. Wannan ma ba shi da amfani.
Alle hans Dage er jo Lidelse, og hans Slid er Græmmelse; end ikke om Natten finder hans Hjerte Hvile. Ogsaa det er Tomhed.
24 Ba abin da mutum zai yi da ya fi yă ci, yă sha, yă ji wa ransa daɗi daga aikinsa. Na lura cewa wannan ma, ya fito daga hannun Allah ne,
Intet er bedre for et Menneske end at spise og drikke og give sin Sjæl gode Dage ved sin Flid. Og det skønnede jeg, at ogsaa det kommer fra Guds Haand.
25 gama in ba tare da shi ba, wa zai iya ci yă sha yă kuma ji daɗi?
Thi hvo kan spise eller drikke uden hans Vilje?
26 Ga wanda ya gamshe shi, Allah yakan ba da hikima da sani da farin ciki, amma ga mai zunubi yakan ba shi aikin tarawa da ajiyar dukiya domin yă miƙa wa wanda ya gamshi Allah. Wannan ma ba shi da amfani, naushin iska ne kawai.
Thi det Menneske, som er godt i hans Øjne, giver han Visdom, Kundskab og Glæde; men den, som synder, giver han Slid med at samle og ophobe for saa at give det til en, som er god i Guds Øjne. Ogsaa det er Tomhed og Jag efter Vind.