< Mai Hadishi 12 >

1 Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
Piemini savu Radītāju savā jaunībā, pirms tās ļaunās dienas nāk un tie gadi tuvojās, kur tu sacīsi: tie man nepatīk.
2 kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
Pirms saule un gaišums un mēnesis un zvaigznes aptumšojās, un padebeši nāk atkal pēc lietus,
3 sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
Tai laikā, kad tie nama sargi trīcēs, un tie stiprie vīri locīsies, un tie malēji stāvēs klusu, tāpēc ka viņu palicis maz, un tie, kas pa logiem skatās, paliks tumši,
4 sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
Un tās divas durvis pret ielu taps aizslēgtas, tā ka malšanas skaņa paliks lēnāka, un viņš uzmostas, kad putniņa balsi dzird, un kad klusu skan visas dziesmas,
5 sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
Kad arī kalnus bīsies un baiļosies, pa ceļu ejot, un kad tas mandeļu koks ziedēs, un sisenis būs par nastu, un līksmība zudīs; jo cilvēks iet uz savu mūža namu, un tie žēlotāji ies apkārt pa ielām;
6 Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
Pirms tā sudraba virve trūks, un tas zelta trauks saplīst un tas smeļamais pie avota izkalst, un tas skritulis pie akas salūst;
7 turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
Jo pīšļiem būs atkal zemē griezties, kā tie ir bijuši, un garam atkal pie Dieva, kas to ir devis.
8 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
Niecība vien! saka tas mācītājs, viss ir niecība!
9 Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
Nu vēl atliek: šis mācītājs bija gudrs, un viņš ļaudīm mācīja atzīšanu, un sadomāja un izmeklēja un sastādīja daudz sakāmus vārdus.
10 Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
Tas mācītājs meklēja, skaistus vārdus atrast un taisnības vārdus pareizi sarakstīt.
11 Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
Gudru vīru vārdi ir kā dzenuļi, un kā iesistas naglas viņu (atziņas) krājumi, no viena Gana doti.
12 Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
Un beidzot: sargies, mans dēls! Grāmatu rakstīšanai nav gala un daudz lasīšanas nopūlē miesu.
13 Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
Visas mācības gala vārds ir šis: bīsties Dievu un turi Viņa baušļus, jo tas pienākas visiem cilvēkiem.
14 Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.
Jo Dievs ikkatru darbu vedīs tiesā līdz ar visu, kas ir apslēpts, vai tas labs vai ļauns.

< Mai Hadishi 12 >