< Mai Hadishi 12 >

1 Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
Souviens-toi de ton Créateur dans les jours de ta jeunesse avant que vienne le temps de l’affliction, et qu’approchent les années dont tu diras: Elles ne me plaisent pas;
2 kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
Avant que le soleil s’obscurcisse, ainsi que la lumière, la lune et les étoiles, et que retournent les nuées après la pluie:
3 sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
Lorsque les gardes de la maison seront ébranlés, et que chancelleront les hommes les plus forts; que celles qui ont accoutumé de moudre seront oisives et en petit nombre, et que seront couverts de ténèbres ceux qui regardaient par les trous;
4 sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
Et qu’on fermera les portes sur la rue, à la faible voix de celle qui moud; et qu’on se lèvera à la voix de l’oiseau, et que deviendront sourdes toutes les filles du chant.
5 sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
On craindra aussi les lieux élevés, et on s’épouvantera dans la voie. L’amandier fleurira, la sauterelle engraissera, le câprier se dissipera; parce que l’homme s’en ira dans la maison de son éternité, et les pleureurs parcourront la place publique.
6 Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
Souviens-toi de ton Créateur, avant que le cordon d’argent se rompe, et que la bandelette d’or se retire, et que la cruche se brise sur la fontaine, et que la roue se rompe sur la citerne;
7 turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
Et que la poussière retourne dans la terre d’où elle était sortie, et que l’esprit revienne à Dieu qui l’a donné.
8 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
Vanité des vanités, dit l’Ecclésiaste, et tout est vanité.
9 Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
Et comme l’Ecclésiaste était très sage, il enseigna le peuple, et raconta ce qu’il avait fait; et dans ses recherches, il composa un grand nombre de paraboles.
10 Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
Il chercha des paroles utiles, et écrivit des discours très justes et pleins de vérité.
11 Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
Les paroles des sages sont comme des aiguillons, comme des clous profondément enfoncés, lesquelles, avec le conseil des maîtres, ont été données par un seul pasteur.
12 Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
Ne recherche rien de plus, mon fils. Il n’y a point de fin à multiplier les livres: et une fréquente méditation est l’affliction de la chair.
13 Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
Écoutons tous pareillement la fin de ce discours. Crains Dieu, et observe ses commandements; car c’est là tout l’homme;
14 Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.
Quant à toutes les choses qui se font, Dieu les appellera en jugement, pour tout ce qui aura été commis par erreur, que ce soit bien ou mal.

< Mai Hadishi 12 >