< Mai Hadishi 12 >

1 Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
Also call to mind your Creator in the days of your youth, before the days of difficulty come, and before the years arrive when you say, “I have no pleasure in them,”
2 kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
do this before the light of the sun and the moon and the stars grows dark, and dark clouds return after the rain.
3 sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
That will be the time when the palace guards will tremble, and strong men are bent over, and the women who grind cease because they are few, and those who look out of windows no longer see clearly.
4 sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
That will be the time when the doors are shut in the street, and the sound of grinding stops, when men are startled at the voice of a bird, and the singing of girls' voices fades away.
5 sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
That will be the time when men become afraid of heights and of dangers along on the road, and when the almond tree blossoms, and when grasshoppers drag themselves along, and when natural desires fail. Then man goes to his eternal home and the mourners go down the streets.
6 Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
Call to mind your Creator before the silver cord is cut, or the golden bowl is crushed, or the pitcher is shattered at the spring, or the water wheel is broken at the well,
7 turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
before the dust returns to the earth where it came from, and the spirit returns to God who gave it.
8 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
“A mist of vapor,” says the Teacher, “everything is vanishing vapor.”
9 Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
The Teacher was wise and he taught the people knowledge. He studied and contemplated and set in order many proverbs.
10 Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
The Teacher sought to write using vivid, upright words of truth.
11 Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
The words of wise people are like goads. Like nails driven deeply are the words of the masters in collections of their proverbs, which are taught by one shepherd.
12 Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
My son, be aware of something more: the making of many books, which has no end and much study brings weariness to the body.
13 Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
The end of the matter after everything has been heard, is that you must fear God and keep his commandments, for this is the whole duty of mankind.
14 Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.
For God will bring every deed into judgment, along with every hidden thing, whether it is good or evil.

< Mai Hadishi 12 >