< Mai Hadishi 12 >

1 Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin ƙuruciyarka, kafin lokacin wahala ta zo shekaru kuma su ƙarato sa’ad da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu,”
Remember, also, thy Creator in the days of thy youth, before the evil days come, and the years draw nigh, of which thou shalt say, “I have no pleasure in them;”
2 kafin rana da haske wata da taurari su daina haske, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙa ruwa;
before the sun, and the light, and the moon, and the stars become dark, and the clouds return after the rain;
3 sa’ad da masu tsaron gida suke rawar jiki, majiya ƙarfi kuma suka rasa ƙarfi, sa’ad da masu niƙa suka daina don ba su da yawa, idanun da suke duba ta taga suka duhunta;
at the time when the keepers of the house tremble, and the strong men bow themselves, and the grinders cease because they are few, and those that look out of the windows are darkened;
4 sa’ad da aka rufe ƙofofin shiga tituna ƙarar niƙa kuma ya tsagaita; sa’ad da kukan tsuntsaye ta farkar da mutane, ba a kuwa jin waƙoƙinsu,
when the doors are shut in the streets, while the sound of the mill is low; when they rise up at the voice of the bird, and all the daughters of music are brought low;
5 sa’ad da mutane suke jin tsoron tudu da kuma hatsarori a tituna; sa’ad da itacen almon ya toho, fāra kuma ya yi ta jan jikinsa da ƙyar, sha’awace-sha’awace sun kafe. Daga nan mutum ya tafi madawwamiyar gidansa ya bar masu makoki suna ta yi.
when also they are afraid of that which is high, and terrors are in the way, and the almond is despised, and the locust is a burden, and the caper-berry is powerless; since man goeth to his eternal home, and the mourners go about the streets; —
6 Ka tuna da shi, kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe; kafin tulu yă ragargaje a maɓulɓula, ko guga ta tsinke a rijiya,
before the silver cord be snapped asunder, and the golden bowl be crushed, or the bucket broken at the fountain, or the wheel shattered at the well,
7 turɓaya ta koma ƙasar da ta fito, rai kuma yă koma ga Allah wanda ya ba da shi.
and the dust return to the earth as it was, and the spirit return to God who gave it.
8 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami, “Gaba ɗaya ba amfani!”
Vanity of vanities, saith the Preacher; all is vanity!
9 Ba kawai Malami ya kasance mai hikima ba, amma kuma ya koyar da mutane. Ya yi tunani ya kuma yi binciken da ya tsara karin magana masu yawa.
Moreover, because the Preacher was wise, he still taught the people knowledge; yea, he considered, and sought out, and set in order, many proverbs.
10 Malami ya yi bincike don yă sami kalmomin da suka dace, kuma abin da ya rubuta daidai ne da kuma gaskiya.
The Preacher sought to find out acceptable words, and to write correctly words of truth.
11 Kalmomin masu hikima kamar tsinken tsokanar dabba ne, tarin maganganunsu kuma kamar ƙusoshi ne da aka kafa daram, da aka ba wa Makiyayi guda.
The words of the wise are as goads; yea, as nails driven in are the words of members of assemblies, given by one shepherd.
12 Ka yi hankali ɗana, game da duk wani ƙari a kan waɗannan. Wallafa littattafai ba shi da iyaka, kuma yawan karatu yakan gajiyar da jiki.
And, moreover, by these, my son, be warned! To the multiplying of books there is no end, and much study wearieth the flesh.
13 Yanzu an ji kome; ga ƙarshen magana. Ka ji tsoron Allah ka kuma kiyaye umarnansa, gama wannan shi ne dukan hakkin mutum.
Let us hear the end of the whole discourse! Fear God and keep his commandments! For this is the duty of every man.
14 Gama Allah zai shari’anta kowane irin aiki, har da waɗanda aka yi a ɓoye, ko nagari ne, ko mugu.
For God will bring every work into the judgment which there is upon every secret thing, whether it be good, or whether it be evil.

< Mai Hadishi 12 >