< Mai Hadishi 11 >

1 Ka jefa burodinka a bisa ruwaye, gama bayan kwanaki masu yawa, za ka sāke samunsa.
Give generously to others [some of] the money [MET] that you have; if you do that, later you will get back an equal amount.
2 Ka raba abin hannunka ga mutum bakwai, I, har ma takwas, gama ba ka san bala’in da zai auko wa ƙasar ba.
Share some of what you have with (seven or eight/several) [others], because you do not know when you will experience a disaster, [and if you give some of what you have to others], [when you experience that disaster, they will kindly help you].
3 In gizagizai sun cika da ruwa, sukan zub da ruwan sama bisa duniya. Itace ya fāɗi, ko wajen kudu ne, ko wajen arewa, inda ya fāɗi a nan zai kwanta.
[It is always true that] when clouds are full of water, they pour rain on the earth. [Similarly], wherever a tree falls on the ground, that is where it will remain.
4 Duk mai la’akari da iska, ba zai yi shuka ba, mai la’akari da gizagizai kuma, ba zai yi girbi ba.
If farmers see in what direction the wind is blowing, they will know whether it is wise at that time to plant things or not. [It is also true that] if farmers look at the clouds [and see that they are blowing from the west, which means that it will probably rain, ] they will not [try to] harvest their crops on that day.
5 Kamar yadda ba ka san hanyar iska ba, ko yadda aka siffanta jiki a cikin mahaifiya, haka ba za ka fahimci aikin Allah Mahaliccin dukan abubuwa ba.
We do not know where the wind comes from or where it goes, and we do not know how bodies are formed in women’s wombs. Similarly [SIM], God is the one who made everything, and we cannot [fully] understand what God does.
6 Ka shuka irinka da safe, da yamma kuma kada ka janye hannunka, gama ba ka san wanda zai yi albarka ba, ko wannan ko wancan, ko kuma duka biyunsu su yi albarka.
[Start] planting your seeds in the morning, and do not stop planting them until the evening, because you do not know which ones will grow better, the ones you plant in the morning or the ones you plant later in the day, or whether both will grow well.
7 Haske da yana da kyau, abu mai kyau ne kuma idanu su dubi rana.
It is very delightful to be alive and see [MTY] the sun [rise every morning].
8 Kome tsawon rayuwar mutum, bari yă more su duka. Amma bari kuma yă tuna da kwanakin duhu, gama su ma za su yi yawa. Duk abin da zai faru ba shi da amfani.
[Even] if people live for many years, they should enjoy all of them. But they should not forget that [some day they will die] and then they will never be able to see any light again, and we do not know what will happen to us after we die.
9 Ka yi murna, kai matashi, a ƙuruciyarka, bari zuciyarka kuma tă yi farin ciki a kwanakin ƙuruciyarka. Ka bi shawarar zuciyarka da kuma duk abin da idanunka suka gani, amma ka sani fa, cikin dukan al’amuran nan Allah zai shari’anta ka.
You young people, be happy while you are still young. Enjoy [IDM] doing the things that you want to do. But do not forget that [some day] God will judge you concerning all the things that you do.
10 Saboda haka, ka fid da tsoro daga zuciyarka ka kakkaɓe duk wani abin da ya dami rayuwarka, gama ƙuruciya da ƙarfi ba su da amfani.
[So when you are young] [MTY], do not worry about anything, and do not pay attention to the pains that you have in your body, because we will not remain young and strong forever.

< Mai Hadishi 11 >