< Mai Hadishi 10 >
1 Kamar yadda matattun ƙudaje sukan ɓata ƙanshin turare, haka’yar wauta takan ɓata hikima da daraja.
Njengoba impukane ezifele phakathi kwamakha ziwenza anuke kubi, kunjalo lobuwula obuncinyane bugabhela ukuhlakanipha lodumo.
2 Zuciyar mai hikima takan karkata ga yin abin da yake daidai, amma zuciyar wawa takan karkata ga yin mugun abu.
Inhliziyo yolungileyo ikhungathekela ekulungeni, kodwa inhliziyo yesiwula ikhungathekela ebubini.
3 Ko yayinda yake tafiya a kan hanya wawa yakan nuna cewa ba shi da hankali, yakan nuna wa kowa wawancinsa.
Loba ehamba nje emgwaqweni oyisiwula kalangqondo, utshengisa loba ngubani ubuphukuphuku bakhe.
4 In hankalin mai mulki ya tashi game da kai, kada ka bar inda kake, gama kwantar da hankali yakan sa a yafe manyan laifofi.
Aluba umbusi ekuthukuthelela, ungasuki esikhundleni sakho; ukuthobeka kungathoba umonakalo obungaba khona.
5 Akwai muguntar da na gani a duniya, irin kuskuren da yake fitowa daga masu mulki.
Bukhona ububi esengibubonile ngaphansi kwelanga, kuliphutha elenziwa ngumbusi:
6 Akan sa wawaye a manyan matsayi, yayinda masu arziki suna ƙarƙashi.
Iziwula ziphakanyiselwa ezikhundleni ezinengi eziphezulu, kodwa abanothileyo belezikhundla eziphansi.
7 Na taɓa ganin bayi a kan dawakai, yayinda’ya’yan sarki suna takawa a ƙasa kamar bayi.
Sengibone izichaka zigade amabhiza, kuthi amakhosana ahambe ngezinyawo njengezichaka.
8 Duk wanda ya haƙa rami shi ne zai fāɗa a ciki; duk wanda ya rushe katanga, shi maciji zai sara.
Lowo ogebha umgodi angawela kuwo; odiliza umduli angalunywa yinyoka.
9 Duk mai farfasa duwatsu shi za su yi wa rauni; duk mai faskaren itace yana cikin hatsarinsu.
Oqhekeza amatshe angalinyazwa yiwo; obanda inkuni angaba sengozini yazo.
10 In gatari ya dakushe ba a kuma wasa shi ba, dole a yi amfani da ƙarfi da yawa, amma ƙwarewa yana kawo nasara.
Lapho ihloka libuthundu ubukhali balo bungalolwanga, kudingeka amandla amanengi kodwa ubungcitshi buyaphumelelisa.
11 In maciji ya sari mutum kafin a ba shi makarin gardi, ina amfanin maganin?
Nxa inyoka ihle ilume ingakalunjwa, umlumbi kaselanzuzo.
12 Kalmomi daga bakin mai hikima alheri ne, amma maganganun wawa za su hallaka shi.
Amazwi aphuma emlonyeni wesihlakaniphi amnandi, kodwa isiwula sichithwa yizindebe zaso.
13 Farkon maganarsa wauta ce, ƙarshenta kuma takan zama muguwar hauka,
Ekuqaleni amazwi aso ayibuwula; ekucineni aseyikuwumana okubi
14 wawa kuma yakan yi ta surutu. Ba wanda ya san abin da zai zo wa zai iya faɗa masa abin da zai faru bayan rasuwarsa?
njalo isiwula sanda ngamazwi. Kakho okwaziyo okuzayo ngubani ongamazisa okuzakwenzakala ngemva kwakhe na?
15 Aikin wawa yakan gajiyar da shi, har bai san hanyar zuwa gari ba.
Umtshikatshika wesiwula uyasidinisa; kasiyazi indlela eya edolobheni.
16 Kaitonki, ya ke ƙasa wadda sarkinki bawa ne wadda kuma hakimanta ke ta shagali tun da safe.
Maye kuwe, wena lizwe onkosi yalo yayiyisichaka, amakhosana akho azitika ngamadili ekuseni.
17 Mai albarka ce, ya ke ƙasa wadda sarkinki haifaffen gidan sarauta ne, wadda hakimanta suke samun abincinsu a daidai lokacin don samun ƙarfi ba don buguwa ba.
Ubusisiwe wena, wena lizwe onkosi yalo izalwa esikhosini amakhosana alo adla ngezikhathi eziqondileyo edlela ukuqina hatshi ukudakwa.
18 In mutum rago ne, sai tsaiko yă lotsa, in hannuwansa ba masa yin kome, ɗaki yakan yi yoyo.
Nxa indoda ilivila intungo ziyabhensa; nxa izandla zayo ziyekethisa indlu iyavuza.
19 Akan shirya abinci don jin daɗi, ruwan inabi kuwa don faranta zuciya, amma kuɗi ne amsar kome.
Idili lenzelwa ukujabula, lewayini lenza impilo ibe mnandi, kodwa imali yiyo impendulo yakho konke.
20 Kada ka zagi sarki ko da a cikin tunaninka ne, ko ka zagi mai arziki ko da a ɗakin kwananka ne, gama tsuntsun sararin sama zai iya ɗauki maganarka, tsuntsu mai fikafikai zai sanar da abin da ka ce.
Ungayithuki inkosi lasemicabangweni yakho, loba uqalekise abanothileyo loba usendlini yakho yokulala, ngoba mhlawumbe inyoni yasemoyeni ingawathwala amazwi akho, loba inyoni ephaphayo ingayabika okutshoyo.