< Mai Hadishi 10 >

1 Kamar yadda matattun ƙudaje sukan ɓata ƙanshin turare, haka’yar wauta takan ɓata hikima da daraja.
Dead flies make the oil of the perfumer loathsome and corrupt; thus doth a little folly weigh down wisdom and honor.
2 Zuciyar mai hikima takan karkata ga yin abin da yake daidai, amma zuciyar wawa takan karkata ga yin mugun abu.
A wise man's mind is at his right hand; but a fool's mind is at his left.
3 Ko yayinda yake tafiya a kan hanya wawa yakan nuna cewa ba shi da hankali, yakan nuna wa kowa wawancinsa.
Yea, even when the fool walketh in the way, his understanding faileth him, and he saith to every one that he is a fool.
4 In hankalin mai mulki ya tashi game da kai, kada ka bar inda kake, gama kwantar da hankali yakan sa a yafe manyan laifofi.
If the anger of a ruler rise up against thee, leave not thy place! for gentleness pacifieth great offences.
5 Akwai muguntar da na gani a duniya, irin kuskuren da yake fitowa daga masu mulki.
There is an evil which I have seen under the sun; an error which proceedeth from a ruler.
6 Akan sa wawaye a manyan matsayi, yayinda masu arziki suna ƙarƙashi.
Folly is set in many high stations, and the noble sit in a low place.
7 Na taɓa ganin bayi a kan dawakai, yayinda’ya’yan sarki suna takawa a ƙasa kamar bayi.
I have seen servants upon horses, and princes walking as servants on foot.
8 Duk wanda ya haƙa rami shi ne zai fāɗa a ciki; duk wanda ya rushe katanga, shi maciji zai sara.
He that diggeth a pit shall fall into it; and whoso breaketh down a wall, a serpent shall bite him.
9 Duk mai farfasa duwatsu shi za su yi wa rauni; duk mai faskaren itace yana cikin hatsarinsu.
Whoso removeth stones shall be hurt therewith, and he that cleaveth wood shall be endangered thereby.
10 In gatari ya dakushe ba a kuma wasa shi ba, dole a yi amfani da ƙarfi da yawa, amma ƙwarewa yana kawo nasara.
If the iron be blunt, and one do not whet the edge, then must he put forth more strength; but an advantage for giving success hath wisdom.
11 In maciji ya sari mutum kafin a ba shi makarin gardi, ina amfanin maganin?
If a serpent bite before he is charmed, then there is no advantage to the charmer.
12 Kalmomi daga bakin mai hikima alheri ne, amma maganganun wawa za su hallaka shi.
The words of a wise man's mouth are gracious; but the lips of a fool are his destruction.
13 Farkon maganarsa wauta ce, ƙarshenta kuma takan zama muguwar hauka,
The beginning of the words of his mouth is folly, and the end of his talk is mischievous madness.
14 wawa kuma yakan yi ta surutu. Ba wanda ya san abin da zai zo wa zai iya faɗa masa abin da zai faru bayan rasuwarsa?
A fool also multiplieth words, though no man knoweth what shall be; and who can tell him what shall be after him?
15 Aikin wawa yakan gajiyar da shi, har bai san hanyar zuwa gari ba.
The labor of the foolish man wearieth him, because he knoweth not how to go to the city.
16 Kaitonki, ya ke ƙasa wadda sarkinki bawa ne wadda kuma hakimanta ke ta shagali tun da safe.
Woe to thee, O land, when thy king is a child, and thy princes feast in the morning!
17 Mai albarka ce, ya ke ƙasa wadda sarkinki haifaffen gidan sarauta ne, wadda hakimanta suke samun abincinsu a daidai lokacin don samun ƙarfi ba don buguwa ba.
Happy thou, O land, when thy king is a noble, and thy princes eat in due season, for strength, and not for drunkenness!
18 In mutum rago ne, sai tsaiko yă lotsa, in hannuwansa ba masa yin kome, ɗaki yakan yi yoyo.
By much slothfulness the building decayeth; and by the slackness of the hands the house leaketh.
19 Akan shirya abinci don jin daɗi, ruwan inabi kuwa don faranta zuciya, amma kuɗi ne amsar kome.
A feast is made for laughter, and wine makes merry; but money answereth all things.
20 Kada ka zagi sarki ko da a cikin tunaninka ne, ko ka zagi mai arziki ko da a ɗakin kwananka ne, gama tsuntsun sararin sama zai iya ɗauki maganarka, tsuntsu mai fikafikai zai sanar da abin da ka ce.
Curse not the king; no, not in thy thought; and curse not the rich in thy bed-chamber! for a bird of the air shall carry the voice; and that which hath wings shall tell the matter.

< Mai Hadishi 10 >