< Mai Hadishi 1 >

1 Kalmomin Malami, ɗan Dawuda, Sarki a Urushalima.
THE WORDS OF the Koheleth, the son of David, king in Jerusalem.
2 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami. “Gaba ɗaya ba amfani! Kome ba shi da amfani!”
Vanity of vanities, saith Koheleth; vanity of vanities, all is vanity.
3 Wace riba ce mutum yake samu daga wahalar da yake fama a duniya?
What profit hath man of all his labour wherein he laboureth under the sun?
4 Zamanai sukan zo zamanai su wuce, amma duniya tana nan har abada.
One generation passeth away, and another generation cometh; and the earth abideth for ever.
5 Rana takan fito rana ta kuma fāɗi, ta kuma gaggauta zuwa inda takan fito.
The sun also ariseth, and the sun goeth down, and hasteth to his place where he ariseth.
6 Iska takan hura zuwa kudu ta kuma juya zuwa arewa; tă yi ta kewayewa, tă yi ta koma inda take fitowa.
The wind goeth toward the south, and turneth about unto the north; it turneth about continually in its circuit, and the wind returneth again to its circuits.
7 Dukan rafuffuka sukan gangara zuwa teku, duk da haka teku ba ya cika. Daga inda rafuffukan suke fitowa, a can suke komawa kuma.
All the rivers run into the sea, yet the sea is not full; unto the place whither the rivers go, thither they go again.
8 Dukan abubuwa suna kawo gajiya, gaban magana. Ido ba ya gaji da gani, haka ma kunne yă ƙoshi da ji.
All things toil to weariness; man cannot utter it, the eye is not satisfied with seeing, nor the ear filled with hearing.
9 Abin da ya taɓa kasancewa, zai sāke kasance, abin da aka yi za a sāke yi kuma; babu wani abu sabo a duniya.
That which hath been is that which shall be, and that which hath been done is that which shall be done; and there is nothing new under the sun.
10 Akwai wani abin da za a ce, “Duba! Ga wani abu sabo”? Abin yana nan, tun dā can, ya kasance kafin lokacinmu.
Is there a thing whereof it is said: 'See, this is new'? — it hath been already, in the ages which were before us.
11 Ba a tunawa da mutanen dā, haka su ma da ba a haifa ba tukuna waɗanda za su biyo bayansu ba za a tuna da su ba.
There is no remembrance of them of former times; neither shall there be any remembrance of them of latter times that are to come, among those that shall come after.
12 Ni, Malami, sarki ne bisa Isra’ila a Urushalima.
I Koheleth have been king over Israel in Jerusalem.
13 Na dauri aniyata in gwada don in bincika ta wurin hikima dukan abin da ake yi a duniya. Kaya mai nauyi ne Allah ya ɗora a kan mutane!
And I applied my heart to seek and to search out by wisdom concerning all things that are done under heaven; it is a sore task that God hath given to the sons of men to be exercised therewith.
14 Na ga dukan abubuwan da ake yi a duniya, dukansu ba su da amfani, naushin iska ne kawai.
I have seen all the works that are done under the sun; and, behold, all is vanity and a striving after wind.
15 Abin da yake tanƙwararre ba zai miƙu ba; ba za a kuma iya ƙidaya abin da ba shi ba.
That which is crooked cannot be made straight; and that which is wanting cannot be numbered.
16 Na yi tunani a raina na ce, “Duba, na yi girma, na kuma ƙaru da hikima fiye da duk wanda ya taɓa mulki a bisa Urushalima kafin ni; na ɗanɗana hikima mai yawa da kuma ilimi.”
I spoke with my own heart, saying: 'Lo, I have gotten great wisdom, more also than all that were before me over Jerusalem'; yea, my heart hath had great experience of wisdom and knowledge.
17 Sa’an nan na ɗaura aniyata ga fahimtar hikima, in kuma san bambanci tsakanin hauka da wauta, amma na koyi cewa wannan ma, naushin iska ne kawai.
And I applied my heart to know wisdom, and to know madness and folly — I perceived that this also was a striving after wind.
18 Gama yawan hikima yakan kawo yawan baƙin ciki; yawan sani, yawan ɓacin rai.
For in much wisdom is much vexation; and he that increaseth knowledge increaseth sorrow.

< Mai Hadishi 1 >