< Maimaitawar Shari’a 1 >
1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
These are the words which Moses spoke unto all Israel on this side of the Jordan, in the wilderness, in the plain opposite Suph, between Paran, and Tophel, and Laban, and Chazeroth, and Di-zahab.
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
It is a journey of eleven days from Horeb by the way of mount Seir unto Kadesh-barnea'.
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
And it came to pass in the fortieth year, in the eleventh month, on the first day of the month, that Moses spoke unto the children of Israel, according to all that the Lord had commanded him concerning them;
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
After he had smitten Sichon the king of the Emorites, who dwelt in Cheshbon, and 'Og the king of Bashan, who dwelt at 'Ashtaroth in Edre'i.
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
On this side of the Jordan, in the land of Moab, began Moses to explain this law, saying,
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
The Lord our God spoke unto us in Horeb, saying, Ye have tarried long enough at this mount;
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
Turn you, and take your journey, and go to the mountain of the Emorites, and unto all its neighboring places, in the plain, in the mountain, and in the lowlands, and in the southern country, and by the coast of the sea, to the land of the Canaanites, and unto the Lebanon, up to the great river, the river Euphrates.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
Behold, I have given up the land before you: go in and take possession of the land which the Lord hath sworn unto your fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give it unto them and to their seed after them.
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
And I said unto you at that time, as followeth, I am not able alone to bear you:
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
The Lord your God hath multiplied you, and, behold, ye are this day as the stars of heaven for multitude.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
May the Lord the God of your fathers make you a thousand times as many more as ye are; and bless you, as he hath spoken unto you.
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
How can I by myself alone bear your cumbrance, and your burden, and your strife!
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
Furnish for yourselves wise and understanding men, and those known among your tribes, and I will place them as chiefs over you.
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
And ye answered me, and said, The thing which thou hast spoken is good to do.
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
And I took the chiefs of your tribes, wise and known men, and I set them as heads over you, captains over thousands, and captains over hundreds, and captains over fifties, and captains over tens, and as officers for your tribes.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
And I commanded your judges at that time, saying, Hear the causes between your brethren, and judge righteously, between a man and his brother, and between his stranger.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
Ye shall not respect persons in judgment; the small as well as the great shall ye hear; ye shall not be afraid of any man; for the judgment belongeth to God: and the cause that is too hard for you shall ye bring unto me, and I will hear it.
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
And I commanded you at that time all the things which ye should do.
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
And we departed from Horeb, and we went through all that great and terrible wilderness, which ye have seen, by the way of the mountain of the Emorites, as the Lord our God had commanded us; and we came as far as Kadesh-barnea'.
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
And I said unto you, Ye are come unto the mountain of the Emorites, which the Lord our God doth give unto us.
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
Behold, the Lord thy God hath given up the land before thee: go up and take possession of it, as the Lord the God of thy fathers hath spoken unto thee; do not fear, and be not discouraged.
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
And ye all came near unto me and said, Let us send out men before us, that they may search out for us the land, and bring us word again concerning the way by which we must go up, and the cities to which we shall come.
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
And the thing was pleasing in my eyes; and I took of you twelve men, one man for every tribe:
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
And they turned and went up into the mountain, and came unto the valley of Eshcol, and spied it out.
25 Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
And they took in their hand some of the fruit of the land, and brought it down unto us; and they brought us word again, and said, The land which the Lord our God doth give us is good.
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
But you would not go up, and ye rebelled against the order of the Lord your God;
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
And ye murmured in your tents, and said, On account of the hatred of the Lord toward us, hath he brought us forth out of the land of Egypt, to deliver us into the hand of the Emorites, to destroy us.
28 Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
Whither shall we go up? our brethren have made faint our heart, saying, The people is greater and taller than we; the cities are great and fortified up to heaven; and moreover the sons of the 'Anakim have we seen there.
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
And I said unto you, Have no dread, nor be ye afraid of them.
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
The Lord your God who goeth before you, he it is who will fight for you; all just as he did for you in Egypt before your eyes;
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
And in the wilderness which thou hast seen, where the Lord thy God bore thee, as a man doth bear his son, on all the way that ye have gone, until ye came unto this place.
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
Yet in this thing do ye not believe in the Lord your God,
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
Who goeth before you on the way to seek out for you a place for your encamping, in fire by night, to cause you to see on the way in which ye are to go, and in a cloud by day.
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
And the Lord heard the voice of your words; and he was wroth, and swore, saying,
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
Surely there shall not one of these men of this evil generation see that good land, which I have sworn to give unto your fathers;
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
Save Caleb the son of Yephunneh, he shall see it, and to him will I give the land upon which he hath trodden, and to his children; because he hath wholly followed the Lord.
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
also with me was the Lord angry for your sakes, saying, also thou shalt not go in thither.
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
Joshua the son of Nun, who standeth before thee, he shall go in thither: him encourage; for he shall cause Israel to inherit it.
39 Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
And your little ones, of whom ye said, They will become a prey, and your children who know not this day either good or evil, these shall go in thither; and unto them will I give it, and they shall possess it.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
But as for you, turn you, and take your journey into the wilderness by the way of the Red Sea.
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
And ye answered and said unto me, We have sinned against the Lord; we indeed will go up and we will fight, according to all that the Lord our God hath commanded us; and ye girded on every man his weapons of war, and ye insisted to go up into the mountain.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
And the Lord said unto me, Say unto them, Go not up, and do not fight; for I am not among you; lest ye be smitten before your enemies.
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
And I spoke unto you; but ye would not hear; and ye rebelled against the order of the Lord, and you were presumptuous, and went up into the mountain.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
And the Emorites, who dwelt in that mountain: came out against you, and they pursued you, as the bees do, and they overthrew you in Seir, as far as Chormah.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
And ye returned and wept before the Lord; but the Lord hearkened not to your voice, nor gave ear unto you.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
And ye tarried in Kadesh many days, according unto the days that ye tarried there.