< Maimaitawar Shari’a 1 >

1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
This is the record of what Moses told all the Israelites during their time in the desert to the east of the Jordan. They were in the Arabah near Suph, between Paran on the one side and Tophel, Laban, Hazeroth, and Di-zahab on the other.
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
(It takes eleven days to go from Horeb to Kadesh-barnea by the road that passes Mount Seir.)
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
On the first day of the eleventh month of the fortieth year, Moses recounted to the Israelites everything that the Lord had instructed him to tell them.
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
This happened after he defeated Sihon king of the Amorites, who ruled in Heshbon, and then at Edrei after he defeated Og king of Bashan, who ruled in Ashtaroth.
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
Speaking on the east side of the Jordan in the land of Moab, Moses began to explain these instructions, saying:
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
The Lord our God told us at Horeb: “You have remained here beside this mountain for long enough.
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
Continue your journey and go to the hill country of the Amorites and all their neighbors, into the Jordan Valley, into the hill country, into the foothills, into the Negev, and along the coast to the country of the Canaanites up to Lebanon, as far as the great River Euphrates.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
Look, I'm giving this land to you. Go and take ownership of the land that the Lord promised he would give to your fathers Abraham, Isaac, and Jacob, and to their descendants who would follow them.”
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
That's when I told you, “I can't take responsibility for all of you by myself.
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
The Lord your God has increased your numbers so much that today there are as many of you as there are stars in the sky.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
May the Lord, the God of your forefathers, multiply you a thousand times and bless you as he has promised.
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
But how can I take on all your troubles, burdens, and arguments just by myself?
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
You must choose for yourselves wise, experienced men with good judgment from each of your tribes, and I will put them in charge as your leaders.”
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
You replied to me, saying, “Your proposal is a good one.”
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
So I summoned your tribal leaders, men with good judgment, and put them in charge of you, as commanders and officials for your tribes. Some were responsible for thousands, some for hundreds, some for fifties, and some for tens.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
At the same time I gave strict instructions to your judges: “Hear the cases brought between your brothers, and make sure you are fair when you judge between a man and his brother or a foreigner living among you.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
Don't show any favoritism when you judge—treat the powerful and the common people just the same. Don't let anyone intimidate you, because judgment is done on God's behalf. Bring me any case that is too hard for you, and I will hear it.”
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
This was also the time I instructed you about everything you had to do.
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
Following the orders of the Lord our God, we left Horeb and set off towards the hill country of the Amorites, passing through the whole of the large and terrifying desert that you yourselves have experienced. When we reached Kadesh-barnea,
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
I explained to you, “You have reached the hill country of the Amorites, which the Lord our God is giving to us.
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
Look, the Lord your God has given you the land! Go and take ownership of the land as the Lord, the God of your forefathers, has told you. Don't be frightened or terrified.”
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
Then you all came to me and suggested, “Let's send men on ahead to explore the land and report back to us about what route to take and which towns we'll come across.”
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
It seemed like a good plan to me, so I chose twelve of your men, one from each tribe.
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
They set off and went up into the hill country as far as the Valley of Eshcol, exploring the land.
25 Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
They brought back some of the country's fruit, carrying it down to us, and gave us the report: “The Lord our God is giving us good land.”
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
But you didn't want to go. You rebelled against the instructions of the Lord your God.
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
You complained while you were in your tents and said, “It's because the Lord hates us that he led us out of Egypt in order to hand us over to the Amorites to be wiped out.
28 Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
Where are we going? Our brothers terrified us because they told us: ‘The people are bigger and taller than us; the towns are large, with high walls that reach the sky. We even saw the descendants of the giant Anak there!’”
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
So I told you, “Don't be frightened or scared of them!
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
The Lord your God who leads your way will fight for you in the same way you saw him do for you in Egypt.
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
He did the same in the desert—you saw how the Lord your God carried you like a father carries his son during your whole journey until you arrived here.”
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
Despite all this, you didn't trust the Lord your God,
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
who led you on the journey, present in the fire by night and in the cloud by day, looking to find a place for you to camp and to show you the way to go.
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
When the Lord heard what you were saying, he got angry and swore an oath:
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
“Not a single one of this evil generation will see the good land I promised to give your forefathers,
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
except Caleb, son of Jephunneh. He will see it, and I will give him and his descendants the land he explored, because he was completely committed to the Lord.”
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
The Lord also got angry with me because of you. He told me, “Even you won't enter the country.
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
However, Joshua, son of Nun, your assistant, will enter it. Encourage him, for he will help Israel to occupy the land.
39 Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
Your small children that you claimed would become prisoners, your children who at the time didn't know good from evil, they will be the ones to enter the land that I will give them, and they will occupy it.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
But now turn around and head back into the desert on the road that leads to the Red Sea.”
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
But you answered and told me, “We have sinned against the Lord! We will go and we will fight and we will do everything the Lord our God has ordered us to do.” Then you all picked up your weapons and prepared for battle thinking it would be easy to go and fight in the hill country.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
But the Lord instructed me, “Order them not to go and fight because I won't be with you to prevent you from being defeated by your enemies.”
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
I told you this, but you refused to listen. You defied the instructions of the Lord and arrogantly went to fight in the hill country.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
Then the Amorites living there in the hills came and attacked you. They chased after you like a swarm of bees, killing you all the way from Seir to Hormah.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
You came back to camp and wept before the Lord, but he refused to listen to what you said or to pay attention to you.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
You stayed there in Kadesh for a long time.

< Maimaitawar Shari’a 1 >