< Maimaitawar Shari’a 1 >

1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
These are the words which Moses spake unto all Israel beyond the Jordan in the wilderness, in the Arabah over against Suph, between Paran, and Tophel, and Laban, and Hazeroth, and Di-zahab.
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
It is eleven days’ [journey] from Horeb by the way of mount Seir unto Kadesh-barnea.
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
And it came to pass in the fortieth year, in the eleventh month, on the first day of the month, that Moses spake unto the children of Israel, according unto all that Jehovah had given him in commandment unto them;
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
after he had smitten Sihon the king of the Amorites, who dwelt in Heshbon, and Og the king of Bashan, who dwelt in Ashtaroth, at Edrei.
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
Beyond the Jordan, in the land of Moab, began Moses to declare this law, saying,
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
Jehovah our God spake unto us in Horeb, saying, Ye have dwelt long enough in this mountain:
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
turn you, and take your journey, and go to the hill-country of the Amorites, and unto all [the places] nigh thereunto, in the Arabah, in the hill-country, and in the lowland, and in the South, and by the sea-shore, the land of the Canaanites, and Lebanon, as far as the great river, the river Euphrates.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
Behold, I have set the land before you: go in and possess the land which Jehovah sware unto your fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give unto them and to their seed after them.
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
And I spake unto you at that time, saying, I am not able to bear you myself alone:
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
Jehovah your God hath multiplied you, and, behold, ye are this day as the stars of heaven for multitude.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
Jehovah, the God of your fathers, make you a thousand times as many as ye are, and bless you, as he hath promised you!
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
How can I myself alone bear your cumbrance, and your burden, and your strife?
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
Take you wise men, and understanding, and known, according to your tribes, and I will make them heads over you.
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
And ye answered me, and said, The thing which thou hast spoken is good [for us] to do.
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
So I took the heads of your tribes, wise men, and known, and made them heads over you, captains of thousands, and captains of hundreds, and captains of fifties, and captains of tens, and officers, according to your tribes.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
And I charged your judges at that time, saying, Hear [the causes] between your brethren, and judge righteously between a man and his brother, and the sojourner that is with him.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
Ye shall not respect persons in judgment; ye shall hear the small and the great alike; ye shall not be afraid of the face of man; for the judgment is God’s: and the cause that is too hard for you ye shall bring unto me, and I will hear it.
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
And I commanded you at that time all the things which ye should do.
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
And we journeyed from Horeb, and went through all that great and terrible wilderness which ye saw, by the way to the hill-country of the Amorites, as Jehovah our God commanded us; and we came to Kadesh-barnea.
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
And I said unto you, Ye are come unto the hill-country of the Amorites, which Jehovah our God giveth unto us.
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
Behold, Jehovah thy God hath set the land before thee: go up, take possession, as Jehovah, the God of thy fathers, hath spoken unto thee; fear not, neither be dismayed.
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
And ye came near unto me every one of you, and said, Let us send men before us, that they may search the land for us, and bring us word again of the way by which we must go up, and the cities unto which we shall come.
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
And the thing pleased me well; and I took twelve men of you, one man for every tribe:
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
and they turned and went up into the hill-country, and came unto the valley of Eshcol, and spied it out.
25 Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
And they took of the fruit of the land in their hands, and brought it down unto us, and brought us word again, and said, It is a good land which Jehovah our God giveth unto us.
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
Yet ye would not go up, but rebelled against the commandment of Jehovah your God:
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
and ye murmured in your tents, and said, Because Jehovah hated us, he hath brought us forth out of the land of Egypt, to deliver us into the hand of the Amorites, to destroy us.
28 Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
Whither are we going up? our brethren have made our heart to melt, saying, The people are greater and taller than we; the cities are great and fortified up to heaven; and moreover we have seen the sons of the Anakim there.
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
Then I said unto you, Dread not, neither be afraid of them.
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
Jehovah your God who goeth before you, he will fight for you, according to all that he did for you in Egypt before your eyes,
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
and in the wilderness, where thou hast seen how that Jehovah thy God bare thee, as a man doth bear his son, in all the way that ye went, until ye came unto this place.
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
Yet in this thing ye did not believe Jehovah your God,
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
who went before you in the way, to seek you out a place to pitch your tents in, in fire by night, to show you by what way ye should go, and in the cloud by day.
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
And Jehovah heard the voice of your words, and was wroth, and sware, saying,
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
Surely there shall not one of these men of this evil generation see the good land, which I sware to give unto your fathers,
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
save Caleb the son of Jephunneh; he shall see it; and to him will I give the land that he hath trodden upon, and to his children, because he hath wholly followed Jehovah.
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
Also Jehovah was angry with me for your sakes, saying, Thou also shalt not go in thither:
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
Joshua the son of Nun, who standeth before thee, he shall go in thither: encourage thou him; for he shall cause Israel to inherit it.
39 Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
Moreover your little ones, that ye said should be a prey, and your children, that this day have no knowledge of good or evil, they shall go in thither, and unto them will I give it, and they shall possess it.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
But as for you, turn you, and take your journey into the wilderness by the way to the Red Sea.
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
Then ye answered and said unto me, We have sinned against Jehovah, we will go up and fight, according to all that Jehovah our God commanded us. And ye girded on every man his weapons of war, and were forward to go up into the hill-country.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
And Jehovah said unto me, Say unto them, Go not up, neither fight; for I am not among you; lest ye be smitten before your enemies.
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
So I spake unto you, and ye hearkened not; but ye rebelled against the commandment of Jehovah, and were presumptuous, and went up into the hill-country.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
And the Amorites, that dwelt in that hill-country, came out against you, and chased you, as bees do, and beat you down in Seir, even unto Hormah.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
And ye returned and wept before Jehovah; but Jehovah hearkened not to your voice, nor gave ear unto you.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
So ye abode in Kadesh many days, according unto the days that ye abode [there].

< Maimaitawar Shari’a 1 >