< Maimaitawar Shari’a 9 >

1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Hör, Israel: I dag skall du gå öfver Jordan, att du inkommer till att intaga de folk, som större och starkare äro än du; stora städer, murade upp till himmelen;
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
Ett stort högt folk, Enakims barn, som du känt hafver, af hvilkom du ock hört hafver: Ho kan stå emot Enaks barn?
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
Så skall du veta i dag, att Herren din Gud går framför dig, en förtärande eld; han varder dem förgörandes och nederläggandes för dig, och skall fördrifva dem, och omintetgöra dem snarliga, såsom Herren dig sagt hafver.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Då nu Herren din Gud dem utdrifvit hafver för dig, så säg icke i dino hjerta: Herren hafver mig här infört, till att intaga detta landet för mina rättfärdighets skull; ändock Herren fördrifver Hedningarna för dig, för deras ogudaktighets skull.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
Ty du kommer icke in i landet till att besitta det, för dina rättfärdighet, eller för dins hjertas fromhets skull; utan Herren din Gud fördrifver dessa Hedningarna för deras ogudaktighets skull, på det han skall fullkomna det ord, som Herren dina fäder, Abraham, Isaac och Jacob, svorit hafver.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
Så vet nu, att Herren din Gud icke gifver dig detta goda landet till att intaga för dina rättfärdighets skull; efter du äst ett halsstyft folk.
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Kom ihåg, och förgät icke, huru du Herran din Gud förtörnade i öknene; ifrå den dag att du drog utur Egypti land, tilldess I komne ären till detta rum, hafven I varit Herranom ohörsamme.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Förty i Horeb förtörnaden I Herran, så att Herren för vredes skull ville förgöra eder;
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
Då jag gången var på berget, till att anamma de stentaflor, förbundsens taflor, som Herren gjorde med eder, och jag blef på bergena fyratio dagar, och fyratio nätter, och åt intet bröd och drack intet vatten.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
Och Herren fick mig de två stentaflorna, beskrefna med Guds finger, och derutinnan all ord, som Herren med eder utur elden på berget talat hade, på församlingenes dag.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
Och efter de fyratio dagar och fyratio nätter fick mig Herren de två förbundsens stentaflor.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
Och Herren sade till mig: Statt upp, gack snart ned hädan; ty ditt folk, som du utfört hafver af Egypten, hafver förderfvat det; de äro snarliga trädde ifrå den vägen, som jag hafver budit dem; de hafva gjort sig ett gjutet beläte.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
Och Herren sade till mig: Jag ser, att detta folket är ett halsstyft folk.
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
Låt mig betämma, att jag förgör dem, och utskrapar deras namn under himmelen. Jag vill göra ett starkare och mägtigare folk af dig, än detta är.
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
Och som jag omvände mig, och gick ned af berget, som brann i eld, och hade de två förbundsens taflor i båda mina händer;
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
Då såg jag, och si, då haden I syndat emot Herran edar Gud, så att I haden gjort en gjuten kalf, och voren snarliga trädde ifrå den vägen, den Herren eder budit hade.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
Så tog jag båda taflorna, och kastade dem bort utu båda händerna, och slog dem sönder för edor ögon;
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
Och föll ned för Herran, såsom tillförene, i fyratio dagar, och fyratio nätter; och åt intet bröd, och drack intet vatten, för alla edra synders skull, som I gjort haden; i det I sådant ondt gjorden för Herranom, till att förtörna honom.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
Ty jag fruktade för den vrede och grymhet, der Herren på eder med förtörnad var, så att han ville förgöra eder. Och Herren hörde mig än i den gången.
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
Var ock Herren storliga vred på Aaron, så att han ville förgöra honom; men jag bad ock för Aaron på samma tiden.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
Men edor synd, kalfven som I gjort haden, tog jag och brände upp i elde, och slog sönder honom, och sönderstötte, tilldess han vardt stoft; och kastade stoftet i bäcken, som flyter utaf bergena.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
Sammalunda förtörnaden I ock Herran i Thabeera, och i Massa, och vid de Lustgrifter.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
Och då Herren sände eder ifrå KadesBarnea, och sade: Går ditupp, och tager landet in, som jag eder gifvit hafver; voren I Herrans edars Guds mun ohörsamme, och trodden icke på honom, och lydden icke hans röst;
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
Ty I hafven varit Herranom ohörsamme, så länge som jag eder känt hafver.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
Då föll jag neder för Herran fyratio dagar, och fyratio nätter, som jag der låg; ty Herren sade, att han ville förgöra eder.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
Men jag bad Herran, och sade: Herre, Herre, förderfva icke ditt folk och din arfvedel, hvilket du genom dina stora magt förlossat, och med mägtiga hand utur Egypten fört hafver.
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Kom ihåg dina tjenare Abraham, Isaac och Jacob; se icke på detta folkets hårdhet, och detta folkets ogudaktighet och synd;
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
Att det landet, der du oss utfört hafver, icke skall säga: Herren kunde icke föra dem uti det land, som han dem lofvat hade, och hafver fördenskull fört dem derut, att han var vred på dem, att han skulle dräpa dem i öknene.
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
Förty de äro ditt folk, och din arfvedel, som du med dine stora magt, och med din uträckta arm, utfört hafver.

< Maimaitawar Shari’a 9 >