< Maimaitawar Shari’a 9 >

1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Poslušaj, oh Izrael: ›Danes prečkaš Jordan, da vstopiš in vzameš v last narode, večje in močnejše kakor ti, velika mesta in ograjena do neba,
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
veliko in visoko ljudstvo, otroke Anákovcev, ki jih poznaš in o katerih si slišal reči: ›Kdo lahko stoji pred Anákovimi otroki!‹
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
Razumi torej ta dan, da je Gospod, tvoj Bog, tisti, ki gre preko pred teboj. Kakor požirajoč ogenj jih bo uničil in on jih bo privedel dol, pred tvoj obraz. Tako jih boš pognal ven in jih hitro uničil, kakor ti je rekel Gospod.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Ne govori v svojem srcu, potem ko jih je Gospod, tvoj Bog, spodil izpred tebe, rekoč: ›Zaradi moje pravičnosti me je Gospod privedel, da vzamem v last to deželo, ‹ temveč jih je zaradi zlobnosti teh narodov Gospod pognal izpred tebe.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
Ne greš, da zaradi svoje pravičnosti ali zaradi poštenosti svojega srca vzameš v last njihovo deželo, temveč zaradi zlobnosti teh narodov jih je Gospod, tvoj Bog, pognal izpred tebe in da lahko izpolni besedo, ki jo je Gospod prisegel tvojim očetom, Abrahamu, Izaku in Jakobu.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
Razumi torej, da ti Gospod, tvoj Bog, te dobre zemlje ne daje v posest zaradi tvoje pravičnosti, kajti ti si trdovratno ljudstvo.
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Zapomni si in ne pozabi, kako si v divjini do besa dražil Gospoda, svojega Boga. Od dneva, ko si odšel iz egiptovske dežele, dokler niste prišli na ta kraj, ste bili uporni zoper Gospoda.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Tudi na Horebu ste do besa izzivali Gospoda, tako da je bil Gospod nad vami jezen, da vas uniči.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
Ko sem odšel gor na goro, da prejmem kamniti plošči, torej plošči zaveze, ki jo je Gospod sklenil z vami, potem sem na gori ostal štirideset dni in štirideset noči niti nisem jedel kruha niti pil vode.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
In Gospod mi je izročil dve kamniti plošči, popisani z Božjim prstom. Na njima je bilo napisano glede na vse besede, ki jih je Gospod z vami govoril na gori, iz srede ognja, na dan zbora.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
Ob koncu štiridesetih dni in štiridesetih noči se je pripetilo, da mi je Gospod dal dve kamniti plošči, torej plošči zaveze.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
Gospod mi je rekel: ›Vstani, hitro se spusti od tod, kajti tvoje ljudstvo, ki si jih privedel iz Egipta, se je izpridilo. Hitro so se obrnili proč iz poti, ki sem jim jo zapovedal. Naredili so si ulito podobo.‹
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
Nadalje mi je Gospod spregovoril, rekoč: ›Videl sem to ljudstvo in glej, to je trdovratno ljudstvo.
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
Pusti me pri miru, da jih lahko uničim in njihovo ime izbrišem izpod neba. Iz tebe pa bom naredil narod, mogočnejši in večji kakor oni.‹
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
Tako sem se obrnil in prišel dol z gore in gora je gorela z ognjem in dve tabli zaveze sta bili v mojih dveh rokah.
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
Pogledal sem in glej, grešili ste zoper Gospoda, svojega Boga in si naredili ulito tele. Hitro ste se obrnili proč iz poti, ki vam jo je zapovedal Gospod.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
Vzel sem dve plošči in ju vrgel iz svojih dveh rok ter ju razbil pred vašimi očmi.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
In padel sem dol pred Gospodom, kakor prvič, štirideset dni in štirideset noči. Niti nisem jedel kruha niti nisem pil vode zaradi vseh vaših grehov, ki ste jih z zlobnim početjem zagrešili v Gospodovih očeh, da ga izzivate k jezi.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
Kajti bal sem se jeze in silnega nezadovoljstva, s katerim je bil Gospod ogorčen zoper vas, da vas uniči. Toda Gospod mi je tudi ob tistem času prisluhnil.
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
Gospod je bil zelo jezen nad Aronom, da bi ga uničil, jaz pa sem isti čas molil za Arona.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
Vzel sem vaš greh, tele, ki ste ga naredili in ga sežgal z ognjem in ga poteptal in ga zelo drobno zmlel, dokler ni bil ta majhen kakor prah, in njegov prah sem vrgel v potok, ki se spušča z gore.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
In pri Tabêri, pri Masi in pri Kibrot-Hattaavi ste do besa izzivali Gospoda.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
Podobno, ko vas je Gospod poslal iz Kadeš Barnée, rekoč: ›Pojdite gor in vzemite v last deželo, ki sem vam jo dal.‹ Potem ste se uprli zoper zapoved Gospoda, svojega Boga in mu niste verjeli niti niste prisluhnili njegovemu glasu.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
Od dneva, ko sem vas spoznal, ste bili uporni zoper Gospoda.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
Tako sem padel dol pred Gospodom, štirideset dni in štirideset noči, kakor sem prvič padel dol, ker je Gospod rekel, da vas bo uničil.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
Molil sem torej h Gospodu in rekel: ›Oh Gospod Bog, ne uniči svojega ljudstva in svoje dediščine, ki si jo odkupil preko svoje veličine, ki si jo s svojo mogočno roko privedel iz Egipta.
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Spomni se svojih služabnikov: Abrahama, Izaka in Jakoba. Ne glej na trmoglavost teh ljudi niti k njihovi zlobnosti niti k njihovemu grehu,
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
da ne bi dežela, od koder si nas privedel, rekla: ›Ker jih Gospod ni bil zmožen privesti v deželo, ki jim jo je obljubil in ker jih je sovražil, jih je privedel ven, da jih pobije v divjini.‹
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
Vendar so tvoje ljudstvo in tvoja dediščina, ki si jih izpeljal s svojo mogočno močjo in s svojim iztegnjenim laktom.‹

< Maimaitawar Shari’a 9 >