< Maimaitawar Shari’a 9 >

1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Ecoute, Israël, tu vas passer aujourd'hui le Jourdain, pour entrer chez des nations plus grandes et plus fortes que toi, vers des villes grandes et murées jusqu'au ciel, pour [les] posséder;
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
Vers un peuple grand et haut; [vers] les enfants des Hanakins, que tu connais, et desquels tu as ouï dire: Qui est-ce qui subsistera devant les enfants de Hanak?
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
Sache donc aujourd'hui que l'Eternel ton Dieu, qui passe devant toi, est un feu consumant. C'est lui qui les détruira, et c'est lui qui les abaissera devant toi; tu les déposséderas, et tu les feras périr subitement comme l'Eternel te l'a dit.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Ne dis point en ton cœur quand l'Eternel ton Dieu les aura chassés de devant toi: C'est à cause de ma justice que l'Eternel m'a fait entrer en ce pays pour le posséder; car c'est à cause de la méchanceté de ces nations-là que l'Eternel les va chasser de devant toi.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
Ce n'est point pour ta justice ni pour la droiture de ton cœur, que tu entres en leur pays pour le posséder; mais c'est pour la méchanceté de ces nations-là, que l'Eternel ton Dieu les va chasser de devant toi; et afin de ratifier la parole que l'Eternel a jurée à tes pères, Abraham, Isaac, et Jacob.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
Sache donc que ce n'est point pour ta justice, que l'Eternel ton Dieu te donne ce bon pays pour le posséder; car tu [es] un peuple de col roide.
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Souviens-toi, [et] n'oublie pas que tu as fort irrité l'Eternel ton Dieu dans ce désert, [et] que depuis le jour que vous êtes sortis du pays d'Egypte, jusqu'à ce que vous êtes arrivés en ce lieu-ci, vous avez été rebelles contre l'Eternel.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Même en Horeb vous avez fort irrité l'Eternel; aussi l'Eternel se mit en colère contre vous, pour vous détruire.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
Quand je montai en la montagne pour prendre les Tables de pierre, les Tables de l'alliance que l'Eternel avait traitée avec vous, je demeurai en la montagne quarante jours et quarante nuits, sans manger de pain, et sans boire d'eau.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
Et l'Eternel me donna deux Tables de pierre, écrites du doigt de Dieu, et ce qui y était écrit c'étaient les paroles que l'Eternel avait toutes proférées lorsqu'il parlait avec vous sur la montagne, du milieu du feu, au jour de l'assemblée.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
Et il arriva qu'au bout de quarante jours et de quarante nuits, l'Eternel me donna les deux Tables de pierre, qui sont les Tables de l'alliance.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
Puis l'Eternel me dit: Lève-toi, descends en hâte d'ici; car ton peuple que tu as fait sortir d'Egypte, s'est corrompu; ils se sont bien-tôt détournés de la voie que je leur avais commandée, ils se sont fait une image de fonte.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
L'Eternel me parla aussi, en disant: J'ai regardé ce peuple, et voici; c'est un peuple de col roide.
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
Laisse-moi, et je les détruirai, et j'effacerai leur nom de dessous les cieux, mais je te ferai devenir une nation plus puissante et plus grande que celle-ci.
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
Je me retirai donc, et je descendis de la montagne. Or la montagne était toute en feu, et j'avais les deux Tables de l'alliance en mes deux mains.
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
Puis je regardai, et voici, vous aviez péché contre l'Eternel votre Dieu, et vous vous étiez fait un veau de fonte; vous vous étiez bien-tôt détournés de la voie que l'Eternel vous avait commandée.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
Alors je saisis les deux Tables, je les jetai de mes deux mains, et je les rompis devant vos yeux.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
Puis je me prosternai devant l'Eternel, durant quarante jours et quarante nuits, comme auparavant, sans manger de pain, et sans boire d'eau, à cause de tout votre péché, que vous aviez commis, en faisant ce qui est déplaisant à l'Eternel, afin de l'irriter.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
Car je craignais la colère et la fureur dont l'Eternel était enflammé contre vous pour vous détruire; et l'Eternel m'exauça encore cette fois-là.
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
L'Eternel fut aussi fort irrité contre Aaron pour le détruire, mais je priai en ce même temps-là aussi pour Aaron.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
Puis je pris votre péché que vous aviez fait, [savoir] le veau, et je le brûlai au feu, je le pilai en le broyant bien, jusqu'à ce qu'il fût réduit en poudre, et j'en jetai la poudre au torrent qui descendait de la montagne.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
Vous avez aussi fort irrité l'Eternel en Tabhéra et en Massa, et en Kibrothtaava.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
Et quand l'Eternel vous envoya de Kadès-barné, en disant: Montez, et possédez le pays que je vous ai donné, alors vous vous rebellâtes contre le commandement de l'Eternel votre Dieu, vous ne le crûtes point, et vous n'obéîtes point à sa voix.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
Vous avez été rebelles à l'Eternel dès le jour que je vous ai connus.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
Je me prosternai donc devant l'Eternel durant quarante jours et quarante nuits, durant lesquels je me prosternai, parce que l'Eternel avait dit qu'il vous détruirait.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
Et je priai l'Eternel, et je lui dis: Ô Seigneur Eternel! ne détruis point ton peuple, et ton héritage que tu as racheté par ta grandeur, [et] que tu as retiré d'Egypte, à main forte.
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Souviens-toi de tes serviteurs Abraham, Isaac, et Jacob; ne regarde point à la dureté de ce peuple, ni a sa méchanceté, ni à son péché;
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
De peur que les habitants du pays, dont tu nous as fait sortir, ne disent: Parce que l'Eternel ne les pouvait pas faire entrer au pays dont il leur avait parlé, et parce qu'il les haïssait, il les a fait sortir [d'Egypte] pour les faire mourir en ce désert.
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
Cependant ils sont ton peuple et ton héritage, que tu as tirés [d'Egypte] par ta grande puissance, et à bras étendu.

< Maimaitawar Shari’a 9 >