< Maimaitawar Shari’a 9 >

1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
“You people of Israel, listen to me! You will soon [HYP] cross the Jordan [River]. In the land that you will enter, there are large cities that have very high walls [around them] that [seem to] [HYP] extend up to the sky. There are people-groups in that land that are more numerous and more powerful than you are.
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
Those people are very tall and strong. [Some of them] are giants who are descendants of Anak. You know about them, and you have heard people say that no one [RHQ] can defeat the descendants of Anak.
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
But I want you to know that Yahweh our God will go ahead of you. He will be like a raging/roaring fire. While you advance, he will defeat and destroy them. As a result, you will quickly be able to expel some of them and kill the others, which is what Yahweh promised that you would do.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
“After Yahweh our God has expelled them for you, do not say to yourselves, ‘It is because we are righteous that Yahweh has enabled us to capture this land.’ The truth is that it is because the people in that land are wicked that Yahweh will expel them as you advance.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
[I say again that] it is not because you are righteous or because you do things that are righteous that you will enter and capture that land. It is because those people-groups are very wicked that Yahweh our God will expel them as you advance, and because he intends to do what he vowed to your ancestors Abraham, Isaac, and Jacob that he would do.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
I want you to know that it is not because you are righteous that Yahweh our God is giving you this good/fertile land. I say that because [you are not righteous]; you are a very stubborn [IDM] people.”
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
“Never forget what your ancestors did in the desert that caused Yahweh our God to become angry. From the day that we left Egypt until the day that we arrived here, you and your ancestors have continually rebelled against him.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Even at Sinai [Mountain] your ancestors caused Yahweh to become angry. Because he was very angry, he was ready to get rid of [all of] them.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
When I climbed the mountain to receive from him the stone tablets on which he had written the Ten Commandments that he was giving to them, I stayed there 40 days and nights, and [during that time] I did not eat or drink anything.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
Yahweh gave me the two stone tablets on which he had written [the commandments] with his own fingers. They were the words/commandments that he had spoken to your ancestors from the fire on that mountain, when they were gathered together [at the bottom of the mountain].
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
“At the end of those 40 days and nights, Yahweh gave me those two stone tablets on which he had written those commandments.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
But then he said to me, ‘Go down the mountain immediately, because [the people whom you are leading], the people whom you led out of Egypt, have committed a terrible sin! They have very quickly done what I commanded them not to do. They have made for themselves a metal statue [of a calf to worship].’
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
Then Yahweh said to me, ‘I have been watching these people, and I see that they are very stubborn.
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
So do not try to stop me. I am going to destroy all of them, with the result that no one anywhere will remember (their names [MTY]/that they ever existed). Then I will enable you to become [the ancestor of] a nation that will be more numerous and more powerful than they are.’
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
So I turned and went down the mountain, carrying in my hands the two stone tablets on which the Ten Commandments were [written]. Fire was burning all over the mountain.
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
I looked, and I was shocked to see that your ancestors had committed a [great] sin against Yahweh. They very quickly had begun to do what Yahweh our God had commanded them not to do. They had [requested Aaron to] make for them [a metal image of] a calf [to worship].
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
So while they were watching, I lifted up those two stone tablets and threw them [on the ground], and they broke into pieces.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
Then I (prostrated myself/lay) on the ground in Yahweh’s presence as I had done before, and I did not eat or drink anything for 40 days and nights. I did that because your ancestors had sinned against Yahweh and caused him to become very angry.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
I was afraid/worried that because Yahweh was very angry with them, he would get rid of all of them. [But again I prayed that he would not do that], and again he listened to me [and answered my prayer].
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
Yahweh was also very angry with Aaron [for making that golden calf] and was ready to kill Aaron. But at the same time I prayed for Aaron also, [and Yahweh answered my prayer].
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
Your ancestors had sinned by [requesting Aaron to] make [a metal statue of] a calf. So I took that statue and [I melted it] in a fire and crushed it and ground it into very tiny pieces [HYP]. Then I threw those tiny pieces into the stream that flowed down the mountain.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
Your ancestors also caused Yahweh to become very angry [by what they did] at [places which they named] Taberah, Massah, and Kibroth-Hattaavah.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
And when we were at Kadesh-Barnea, Yahweh said to your ancestors, ‘Go up and capture the land that I am about to give to you!’ But they rebelled against him. They did not trust him, and they did not obey what he told [MTY] them to do.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
Your ancestors rebelled against Yahweh from the first day that I knew them, [in Egypt].
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
So, [as I said], I lay on the ground in Yahweh’s presence for 40 days and nights, because Yahweh had said that he would get rid of your ancestors.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
And I prayed to Yahweh, saying, ‘Lord God, these people belong to you; do not destroy them. They are people whom you rescued and brought out of Egypt by your very great power. [DOU, MTY]
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Do not forget [what you promised to] Abraham, Isaac, and Jacob. Please ignore these stubborn and wicked people and the sin that they have committed.
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
If you do not do that, [and if you get rid of them], the people of Egypt will [hear about it and] say that you were not able to bring them into the land that you promised to give to them. They will say that you took them into the desert only to kill them there because you hated them.
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
[Do not forget that] they are your people. [You chose them to] belong to you. You brought them out [from Egypt] by your very great power [DOU, MTY].’”

< Maimaitawar Shari’a 9 >