< Maimaitawar Shari’a 9 >
1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Hear O Israel! thou art passing, to-day, over the Jordan, to go in to dispossess nations, greater and stronger than thou, —cities great and fortified into the heavens;
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
a people great and tall, the sons of Anakim, —whom, thou, knowest, and of whom thou hast heard say, Who can stand before the sons of Anak?
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
So then, thou must consider to-day, that Yahweh thy God, he it is that is passing over before thee as a consuming fire, he, will destroy them, and, he, will cause them to bow down before thee, —so shalt thou dispossess them, and destroy them speedily, as Yahweh hath spoken unto thee.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Do not speak in thy heart, when Yahweh thy God casteth them out from before thee saying, For mine own righteousness, hath Yahweh brought me in, to possess this land, —whereas it is for the lawlessness of these nations, that, Yahweh, is dispossessing them from before thee.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
Not for thine own righteousness, nor for the uprightness of thine own heart, art thou going in to possess their land, —but for the lawlessness of these nations, is, Yahweh thy God driving them out from before thee, and that he may establish the word which Yahweh sware unto thy fathers, unto Abraham, unto Isaac, and unto Jacob.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
So then, thou must consider that, not for thine own righteousness, is Yahweh thy God giving unto thee this good land to possess it, —for a stiff-necked people, thou art.
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Remember—do not forget, how thou didst provoke Yahweh thy God, in the desert, —yea from the day when thou camest forth out of the and of Egypt until ye entered as far as this place, have ye been quarrelling, with Yahweh.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Even in Horeb, ye provoked Yahweh to wrath, —so that Yahweh showed himself angry with you to destroy you.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
When I went up into the mountain to receive the tables of stone—the tables of the covenant, which Yahweh had solemnised with you, then abode I in the mountain forty days and forty nights, food, did I not, eat, and water, did I not drink.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
Then did Yahweh deliver unto me the two tables of stone, written with the finger of God, —and [there was] upon them, according to all the words which Yahweh had spoken with you in the mountain out of the midst of the fire in the day of the convocation.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
So then it came to pass at the end of forty days and forty nights, that Yahweh gave unto me the two tables of stone the tables of the covenant.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
Then said Yahweh unto me—Up! get down quickly out of this mountain, for thy people whom thou hast brought forth out of Egypt, have broken faith, —they have turned aside quickly, out of the way which I commanded them, —they have made them a molten image.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
And Yahweh spake unto me saying, —I have looked on this people, and lo! a stiff-necked people, it is.
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
Let me alone, that I may destroy them, and wipe out their name from under the heavens, —and make thee into a nation stronger and more in number than they.
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
So I turned, and came down out of the mountain, now the mountain was burning with fire, —and the two tables of the covenant were upon my two hands.
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
Then looked I, and lo! ye had sinned against Yahweh your God, ye had made you a molten calf, —ye had turned aside quickly, out of the way which Yahweh had commanded you.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
So I seized the two tables, and cast them from off my two hands, —and brake them in pieces before your eyes.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
Then lay I prostrate before Yahweh as at the first, forty days and forty nights, food, did I not eat, and water, did I not drink, —because of all your sin which ye had sinned, in doing the thing that was wicked, in the eyes of Yahweh. to provoke him to anger.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
For I shrank with fear from the face of the anger and the hot displeasure, wherewith Yahweh was provoked against you to destroy you, —but Yahweh hearkened unto me, even at that time.
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
And with Aaron, did Yahweh show himself exceedingly angry, to destroy him, —so I prostrated myself, even in behalf of Aaron at that time.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
And your sin which ye had made even the calf, took I and burned it up with fire, and pounded it very small, until it was fine as dust, —then cast I the dust thereof into the torrent that descended out of the mountain.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
Also, at Taberah, and at Massah, and at Kibroth-hataavah, a cause of provocation, became ye unto Yahweh.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
Also when Yahweh sent you out of Kadesh-barnea saying, Go up and possess the land which I have given unto you then quarreled ye with the bidding of Yahweh your God, and trusted him not, neither hearkened unto his voice.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
Ye have been quarrelling, with Yahweh, —from the day that I first knew you.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
Thus, then lay I prostrate before Yahweh, the forty days and the forty nights that I did lie prostrate, —because Yahweh spake of destroying you.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
Therefore I prostrated myself unto Yahweh and said, My Lord Yahweh! Do not destroy thy people even thine inheritance, which thou hast redeemed in thy greatness, —which thou hast brought forth out of Egypt with a firm hand.
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Have remembrance of thy servants, of Abraham, of Isaac and of Jacob, —do not regard the obduracy of this people, or their lawlessness or their sin:
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
lest the land out of which thou hast brought us forth say, Because Yahweh was not able to bring them into the land of which he had spoken to them, —and because he hated them, took he them forth to put them to death in the desert.
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
Yet, they, are thy people and thine inheritance, —whom thou hast brought forth with thy great strength, and with thy stretched-out arm.