< Maimaitawar Shari’a 9 >
1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Hear, O Israel: Thou art to pass this day over the Jordan, to go in to drive out nations greater and mightier than thou, [to conquer] cities great and fortified up to heaven,
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
A people great and tall, the children of the 'Anakim, whom thou knowest, and of whom thou hast heard say, Who can stand before the children of 'Anak!
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
Understand therefore this day, that the Lord thy God it is who goeth over before thee, he is a consuming fire; he will destroy them, and he will subdue them before thy face; and thou wilt drive them out, and destroy them quickly, as the Lord hath spoken unto thee.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Thou must not say in thy heart, when the Lord thy God doth cast them out from before thee, as followeth, For my righteousness hath the Lord brought me in to possess this land; and that for the wickedness of these nations the Lord doth drive them out from before thee.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
Not for thy righteousness, nor for the uprightness of thy heart, dost thou go in to possess their land; but for the wickedness of these nations doth the Lord thy God drive them out from before thee, and in order that he may fulfill the word which the Lord hath sworn unto thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
And thou shalt know, that not for thy righteousness doth the Lord thy God give unto thee this good land to possess it; for thou art a stiff-necked people.
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Remember, do not forget, how thou didst provoke the Lord thy God to wrath in the wilderness: from the day that thou wentest out of the land of Egypt, until ye came unto this place, have ye been rebellious against the Lord.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Also at Horeb ye provoked the Lord to wrath, so that the Lord was angry with you to destroy you.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
When I was gone up into the mount to receive the tables of stone, the tables of the covenant which the Lord had made with you, and I abode on the mount forty days and forty nights, bread did I not eat, and water did I not drink.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
And the Lord gave unto me the two tables of stone inscribed by the finger of God; and on them [was written] according to all the words, which the Lord had spoken with you on the mount out of the midst of the fire on the day of the assembly.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
And it came to pass at the end of forty days and forty nights, that the Lord gave unto me the two tables of stone, the tables of the covenant.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
And the Lord said unto me, Arise, get thee down quickly from here; for thy people which thou hast brought forth out of Egypt have become corrupted; they have quickly turned aside out of the way which I have commanded them; they have made themselves a molten image.
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
And the Lord said unto me, thus, I have seen this people, and, behold, it is a stiff-necked people:
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
Let me alone, and I will destroy them, and blot out their name from under the heavens; and I will make of thee a nation mightier and more numerous than they.
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
And I turned and came down from the mount, and the mount was burning with fire; and the two tables of the covenant were upon my two hands.
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
And I looked, and, behold, ye had sinned against the Lord your God, ye had made yourselves a molten calf; ye had turned aside quickly out of the way which the Lord had commanded you.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
And I took hold of the two tables, and cast them out of my two hands, and I broke them before your eyes.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
And I threw myself down before the Lord, as at the first, forty days and forty nights; bread did I not eat, and water did I not drink; on account of all your sins which ye had committed, in doing what is evil in the eyes of the Lord, to provoke him to anger.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
For I was afraid of the anger and the indignation, wherewith the Lord was wroth against you to destroy you; but the Lord hearkened unto me also at that time.
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
And with Aaron was the Lord very angry to destroy him; and I prayed also for Aaron at the same time.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
And your work of sin, which ye had made, the calf, I took and burnt it in fire, and stamped it, grinding it very small, until it was as fine as dust: and I cast the dust thereof into the brook that descendeth from the mount.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
And at Taberah, and at Massah and at Kibroth-hattaavah, have ye been provoking the Lord to wrath.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
And when the Lord sent you from Kadesh-barnea', saying, Go up and take possession of the land which I have given you: then rebelled ye against the order of the Lord your God, and ye believed not in him, and ye hearkened not to his voice.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
Rebellious have ye been against the Lord, from the day that I have known you.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
And I threw myself down before the Lord those forty days and forty nights, which I threw myself down; because the Lord had said that he would destroy you.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
And I prayed unto the Lord, and said, O Lord Eternal, destroy not thy people and thy heritage, which thou hast redeemed through thy greatness, which thou hast brought forth out of Egypt with a mighty hand.
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Think of thy servants, of Abraham, of Isaac, and of Jacob; turn not unto the stubbornness of this people, nor to its wickedness, nor to its sin:
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
Lest [the inhabitants of] the land whence thou hast brought us out say, Out of want of ability in the Lord to bring them into the land which he had promised them, and out of his hatred to them, hath he brought them out to slay them in the wilderness.
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
Whereas they are thy people and thy heritage, whom thou hast brought out by thy mighty power and by thy outstretched arm.