< Maimaitawar Shari’a 9 >

1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Hør, Israel! Du drager nu over Jordan for at komme og gøre dig til Herre over Folk, der er større og mægtigere end du selv, over store Byer med himmelhøje Fæstningsværker;
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
over et stort Folk, høje som Kæmper, Anakiternes Efterkommere, som du selv kender, og om hvem du selv har hørt sige: Hvem kan holde Stand mod Anakiterne!"
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
Så skal du nu vide, at det er HERREN din Gud, der går foran dig som en fortærende Ild; han vil ødelægge dem, og han vil underku dem for dig, så du kan drive dem bort og ødelægge dem i Hast, således som HERREN har sagt dig.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Når HERREN din Gud jager dem bort foran dig, tænk så ikke: "For min Retfærdigheds Skyld lod HERREN mig komme ind og tage dette Land i Besiddelse!" Thi det er for disse Folks Ugudeligheds Skyld, at HERREN driver dem bort foran dig!
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
Det er ikke for din Retfærdigheds eller dit ædle Hjertes Skyld, du kommer ind og tager deres Land i Besiddelse, nej, det er på Grund af disse Folks Ondskab, at HERREN driver dem bort foran dig, og fordi han vil opfylde det Ord, han tilsvor dine Fædre, Abraham, Isak og Jakob.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
Så vid da, at det ikke er for din Retfærdigheds Skyld, at HERREN din Gud giver dig dette herlige Land i Eje; thi du er et Folk med hårde Halse!
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Kom i Hu, glem ikke, hvorledes du fortørnede HERREN din Gud i Ørkenen! Lige fra den Dag I drog ud af Ægypten, og til I kom til Stedet her, har I været genstridige mod HERREN.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Ved Horeb fortørnede I HERREN, og HERREN blev vred på eder, så han vilde ødelægge eder.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
Da jeg var steget op på Bjerget for at modtage Stentavlerne, den Pagts Tavler, som HERREN havde sluttet med eder, opholdt jeg mig på Bjerget fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter uden at spise eller drikke,
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
og HERREN gav mig de to Stentavler, beskrevne med Guds Finger; og på dem stod alle de Ord, HERREN havde talt til eder på Bjerget ud fra Ilden, den Dag I var forsamlet.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
Da de fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter var omme, gav HERREN mig de to Stentavler, Pagtens Tavler.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
Og HERREN sagde til mig: "Stå op og skynd dig ned herfra, thi det Folk, du førte ud af Ægypten, har handlet ilde; hastigt er de veget fra den Vej, jeg foreskrev dem: de har lavet sig et støbt Billede!"
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
Og HERREN sagde til mig: "Jeg har set dette Folk, og se, det er et Folk med hårde Halse;
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
lad mig i Fred, så jeg kan ødelægge dem og udslette deres Navn under Himmelen; så vil jeg gøre dig til et Folk, mægtigere og større end det!"
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
Da vendte jeg mig bort og steg ned fra Bjerget med Pagtens to Tavler i mine Hænder, medens Bjerget brændte i lys Lue;
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
og jeg så, og se, I havde syndet mod HERREN eders Gud, I havde lavet eder en støbt Tyrekalv; hastigt var I veget fra den Vej, HERREN havde foreskrevet eder.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
Da greb jeg de to Tavler og kastede dem ud af mine Hænder og knuste dem for eders Øjne.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
Og derpå faldt jeg ned for HERRENs Åsyn fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter ligesom forrige Gang, uden at spise eller drikke, for alle eders Synders Skyld, som I havde begået, idet I gjorde, hvad der var ondt i HERRENs Øjne, så I fortørnede ham.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
Thi jeg frygtede for, at HERREN skulde tilintetgøre eder i den Vrede og Harme, som opfyldte ham imod eder. Og HERREN bønhørte mig også den Gang!
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
Også på Aron blev HERREN vred, så han vilde tilintetgøre ham; men den Gang gik jeg også i Forbøn for Aron.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
Men eders syndige Værk, Kalven, tog jeg og brændte; og jeg knuste og malede den til fint Støv, og Støvet kastede jeg i Bækken, som løber ned ad Bjerget.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
Også i Tabera, Massa og Hibrot Hatta'va fortørnede I HERREN.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
Og da HERREN lod eder rejse fra Kadesj Barnea og bød eder drage op og tage det Land i Besiddelse, som han vilde give eder, trodsede I HERREN eders Guds Befaling, og I troede ikke på ham og adlød ham ikke.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
I har været genstridige mod HERREN, så længe jeg har kendt eder.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
Så faldt jeg ned for HERRENs Åsyn i de fyrretyve Dage og fyrretyve Nætter, fordi HERREN havde sagt, at han vilde tilintetgøre eder,
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
og jeg bad til HERREN og sagde: "Herre, HERRE, ødelæg ikke dit Folk og din Ejendom, som du udløste ved din store Magt og førte ud af Ægypten med stærk Hånd!
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Kom dine Tjenere i Hu, Abraham, Isak og Jakob; giv ikke Agt på dette Folks Halsstarrighed, på dets Ugudelighed og på dets Synd,
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
for at man ikke skal sige i det Land, du førte os ud fra: Fordi HERREN ikke evnede at føre dem til det Land, han havde lovet dem, og fordi han hadede dem, derfor førte han dem ud for at lade dem omkomme i Ørkenen!
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
De er jo dit Folk og din Ejendom, som du førte ud ved din store Kraft og din udstrakte Arm!"

< Maimaitawar Shari’a 9 >