< Maimaitawar Shari’a 8 >

1 Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
Prends bien garde de pratiquer tous les préceptes, que moi, je te prescris aujourd’hui, afin que vous puissiez vivre, que vous vous multipliiez, et, qu’après y être entrés, vous possédiez la terre au sujet de laquelle le Seigneur a juré à vos pères.
2 Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
Et tu te souviendras de tout le chemin par lequel le Seigneur ton Dieu t’a conduit pendant quarante ans à travers le désert, pour t’affliger, t’éprouver et faire connaître ce qui se passait dans ton cœur: si tu garderais ses commandements, ou non.
3 Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
Il t’a affligé par la faim, et il t’a donné pour nourriture la manne que tu ignorais, toi, et tes pères, afin de te montrer que ce n’est pas de pain seulement que l’homme vit, mais de toute parole qui sort de la bouche de Dieu.
4 Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
Ton vêtement dont tu étais couvert, n’a pas manqué par la vétusté, et ton pied n’a pas été déchiré en dessous, et voici la quarantième année.
5 Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
C’est afin que tu penses en ton cœur, que comme un homme instruit son fils, ainsi le Seigneur ton Dieu t’a instruit;
6 Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
Afin que tu gardes les commandements du Seigneur ton Dieu, que tu marches dans ses voies, et que tu le craignes.
7 Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
Car le Seigneur ton Dieu t’introduira dans une terre bonne, terre de ruisseaux, d’eaux, et de fontaines, dans les champs et les montagnes de laquelle jaillissent des sources de fleuves.
8 ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
Terre de blé, d’orge et de vignes, dans laquelle naissent les figuiers, les grenadiers et les oliviers; terre d’huile et de miel.
9 ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
Où tu mangeras ton pain sans en manquer jamais, où tu jouiras de l’abondance de toutes choses, dont les pierres sont du fer; et de ses montagnes on exploite des mines d’airain;
10 Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Afin que, lorsque tu auras mangé, et que tu te seras rassasié, tu bénisses le Seigneur ton Dieu pour la terre excellente qu’il t’a donnée.
11 Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
Aie soin, et prends garde de n’oublier jamais le Seigneur ton Dieu, et de ne point négliger ses préceptes, ses ordonnances et ses cérémonies, que moi, je te prescris aujourd’hui;
12 To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
De peur qu’après que tu auras mangé, et que tu seras rassasié, que tu auras bâti de belles maisons, et que tu t’y seras établi,
13 sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
Et que tu auras eu des troupeaux de bœufs, et des troupeaux de brebis, et une abondance d’argent et d’or de toutes choses,
14 to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
Ton cœur ne s’élève, et que tu ne te souviennes plus du Seigneur ton Dieu, qui t’a retiré de la terre d’Egypte, de la maison de servitude;
15 Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
Qui a été ton guide dans le désert grand et terrible, dans lequel étaient des serpents au souffle brûlant, des scorpions et des dipsas, et où il n’y avait absolument aucune eau; qui a fait jaillir des ruisseaux de la pierre la plus dure,
16 Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
Et qui t’a nourri dans le désert d’une manne que n’ont pas connue tes pères. Et après qu’il t’a eu affligé et éprouvé, il a eu enfin pitié de toi,
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
Afin que tu ne dises pas en ton cœur: C’est ma force, et la vigueur de ma main qui m’ont acquis toutes ces choses;
18 Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
Mais que tu te souviennes que c’est le Seigneur ton Dieu lui-même qui t’a donné des forces, afin qu’il accomplît ainsi l’alliance au sujet de laquelle il a juré à tes pères, comme le montre le présent jour.
19 In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
Mais si, oubliant le Seigneur ton Dieu, tu suis des dieux étrangers, et que tu les serves et les adores, voici maintenant que je te prédis que tu périras entièrement.
20 Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.
Comme les nations qu’a détruites le Seigneur à ton entrée, ainsi vous aussi, vous périrez, si vous êtes désobéissants à la voix du Seigneur votre Dieu.

< Maimaitawar Shari’a 8 >