< Maimaitawar Shari’a 8 >

1 Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
Vous observerez et mettrez en pratique tous les commandements que je vous prescris aujourd'hui, afin que vous viviez, que vous multipliiez, que vous entriez dans le pays que l'Éternel a juré à vos pères et que vous le possédiez.
2 Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
Tu te souviendras de tout le chemin que l'Éternel, ton Dieu, t'a fait faire pendant ces quarante années dans le désert, afin de t'humilier, de t'éprouver, de savoir ce que tu avais dans le cœur, si tu garderais ou non ses commandements.
3 Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
Il t'a humilié, t'a laissé avoir faim et t'a nourri de la manne, que tu ne connaissais pas et que tes pères ne connaissaient pas, afin de t'apprendre que l'homme ne vit pas seulement de pain, mais que l'homme vit de toute parole qui sort de la bouche de Yahvé.
4 Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
Ton vêtement n'a pas vieilli sur toi, et ton pied n'a pas enflé, pendant ces quarante années.
5 Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
Tu considéreras dans ton cœur que, comme un homme discipline son fils, ainsi Yahvé ton Dieu te discipline.
6 Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
Tu observeras les commandements de l'Éternel, ton Dieu, pour marcher dans ses voies et pour le craindre.
7 Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
Car l'Éternel, ton Dieu, te fait entrer dans un bon pays, un pays de ruisseaux d'eau, de sources et d'eaux souterraines qui coulent dans les vallées et les collines;
8 ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
un pays de blé, d'orge, de vignes, de figuiers et de grenadiers, un pays d'oliviers et de miel;
9 ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
un pays où tu mangeras du pain sans manquer, où tu ne manqueras de rien; un pays dont les pierres sont du fer, et dans les collines duquel on peut extraire du cuivre.
10 Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Tu mangeras et tu te rassasieras, et tu béniras Yahvé ton Dieu pour le bon pays qu'il t'a donné.
11 Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
Prends garde que tu n'oublies Yahvé, ton Dieu, en n'observant pas ses commandements, ses ordonnances et ses lois, que je te prescris aujourd'hui;
12 To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
de peur que, lorsque tu auras mangé et que tu seras rassasié, lorsque tu auras bâti de belles maisons et que tu y auras habité,
13 sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
lorsque tes troupeaux se seront multipliés, que ton argent et ton or se seront multipliés, et que tout ce que tu possèdes se sera multiplié,
14 to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
ton cœur ne s'élève et tu n'oublies Yahvé, ton Dieu, qui t'a fait sortir du pays d'Égypte, de la maison de servitude;
15 Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
qui t'a conduit à travers un désert grand et terrible, avec des serpents venimeux et des scorpions, et une terre assoiffée où il n'y avait pas d'eau; qui t'a fait couler de l'eau du rocher de silex;
16 Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
qui t'a nourri dans le désert de la manne que tes pères ne connaissaient pas, afin de t'humilier et de t'éprouver, pour te faire du bien à la fin de ta vie;
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
et de peur que tu ne dises dans ton cœur: « C'est ma puissance et la force de ma main qui m'ont procuré ces richesses ». »
18 Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
Mais toi, tu te souviendras de Yahvé ton Dieu, car c'est lui qui te donne le pouvoir d'acquérir des richesses, afin d'établir son alliance, qu'il a jurée à tes pères, comme elle l'est aujourd'hui.
19 In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
Si tu oublies l'Éternel, ton Dieu, et si tu vas après d'autres dieux, si tu les sers et te prosternes devant eux, je témoigne aujourd'hui contre toi que tu périras.
20 Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.
Comme les nations que l'Éternel fait périr devant vous, ainsi vous périrez, parce que vous n'avez pas voulu écouter la voix de l'Éternel, votre Dieu.

< Maimaitawar Shari’a 8 >