< Maimaitawar Shari’a 8 >

1 Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
All the commandment which I am commanding thee to-day, shalt thou, observe, to do, —that ye may, live, and multiply, and enter in and possess the land, which Yahweh sware unto your fathers.
2 Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
So then, thou shalt remember all the way in which Yahweh thy God caused thee to journey these forty years in the desert, —that he might humble thee to put thee to the proof to know what was in thy heart, —whether thou wouldest keep his commandments or not.
3 Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
So he humbled thee, and suffered thee to hunger, and fed thee with manna which thou hadst not known, neither had thy fathers known, —that he might lead thee to consider that not on bread alone, shall the son of earth live, but on whatsoever cometh from the bidding of Yahweh, shall the son of earth live.
4 Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
Thy mantle, hath not fallen with age from off thee, and, thy foot, hath not become swollen, —these forty years.
5 Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
Thou must consider, then with thy heart, —that as a man chasteneth his son, Yahweh thy God, hath been chastening thee.
6 Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
Thou shalt therefore keep the commandments of Yahweh thy God, —to walk in his ways and to revere him.
7 Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
For, Yahweh thy God, is bringing thee into a good land; a land of ravines of water, of fountains and depths, coming forth in valley, and in mountain:
8 ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
a land of wheat and barley, and vine and fig-tree, and pomegranate, —a land of olive oil, and honey:
9 ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
a land wherein not in scarcity, shalt thou eat food, thou shalt lack nothing therein, —a land whose stones are iron, and out of whose hills thou mayest hew copper.
10 Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
So then thou shalt eat and be satisfied, —and bless Yahweh thy God, for the good land which he hath given unto thee.
11 Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
Take heed to thyself, lest thou forget Yahweh thy God, —so as not to keep his commandments and his regulations and his statutes, which I am commanding thee to-day;
12 To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
lest thou eat, and be satisfied, —and goodly houses, thou build and inhabit;
13 sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
and thy herd and thy flock, increase, and silver and gold, increase unto thee, —and all that thou hast, increase;
14 to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
and so thy heart be lifted up, —and thou forget Yahweh thy God, who brought thee forth out of the land of Egypt out of the house of servants;
15 Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
who caused thee to journey through the great and terrible desert, of fiery serpents and scorpions, and thirsty wastes where was no water, —who brought forth for thee water out of the flinty rock;
16 Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
who fed thee with manna in the desert, which thy fathers had not known, —that he might humble thee, and that he might put thee to the proof, to do thee good in thy hereafter,
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
and lest thou shouldest say in thy heart, —Mine own strength and the might of mine own hand, have gotten me this wealth.
18 Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
But thou shalt remember Yahweh thy God, that it was, he, who had been giving thee strength to get wealth, —that so he might establish his covenant which he sware to thy fathers (as at this day).
19 In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
But it shall be if thou forget, Yahweh thy God, and go after ether gods, and serve them, and bow thyself down to them, I testify against you to-day, that ye shall perish:
20 Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.
like the nations which, Yahweh, is causing to perish from before you, so, shall ye perish, because ye would not hearken unto the voice of Yahweh your God.

< Maimaitawar Shari’a 8 >