< Maimaitawar Shari’a 8 >

1 Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
All the commandment which I command thee this day shall ye observe to do; in order that ye may live, and multiply, and go in and take possession of the land which the Lord hath sworn unto your fathers.
2 Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
And thou shalt remember all the way which the Lord thy God hath led thee these forty years in the wilderness, in order to afflict thee, to prove thee, to know what is in thy heart, whether thou wouldst keep his commandments, or not.
3 Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
And he afflicted thee, and suffered thee to hunger, and he gave thee manna to eat, which thou knewest not, and which thy fathers had not known; in order that he might make thee know that not by bread alone man doth live, but by every thing that proceedeth out of the mouth of the Lord doth man live.
4 Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
Thy garment did not fall worn out from thee, and thy foot did not swell, these forty years.
5 Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
And thou shalt consider in thy heart, that, as a man chasteneth his son, so doth the Lord thy God chasten thee.
6 Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
And thou shalt keep the commandments of the Lord thy God, to walk in his ways, and to fear him.
7 Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
For the Lord thy God bringeth thee into a good land, a land of brooks of water, of fountains and depths that spring out of valleys and mountains;
8 ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
A land of wheat, and barley, and of the vine, and the fig-tree, and the pomegranate; a land of the oil-olive, and of honey;
9 ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
A land wherein thou shalt eat bread without scarceness, wherein thou shalt not lack anything; a land the stones whereof are iron, and out of the mountains of which thou canst hew copper.
10 Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
And when thou hast eaten and art satisfied, then shalt thou bless the Lord thy God for the good land which he hath given thee.
11 Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
Take heed unto thyself that thou forget not the Lord thy God, so as not to keep his commandments, and his ordinances, and his statutes, which I command thee this day;
12 To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
That when thou hast eaten and art satisfied, and hast built goodly houses, and dwelt therein;
13 sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
And when thy herds and thy flocks multiply, and thy silver and thy gold are multiplied, and all that thou hast is multiplied:
14 to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
Thy heart be then not lifted up, and thou forget the Lord thy God, who hath brought thee forth out of the land of Egypt, from the house of slavery;
15 Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
Who hath led thee through the great and terrible wilderness, wherein are snakes, poisonous serpents, and scorpions, and drought, where there is no water; who hath brought forth for thee water out of the flinty rock;
16 Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
Who hath fed thee in the wilderness with manna, which thy fathers knew not; in order to afflict thee, and in order to prove thee, to do thee good at thy latter end;
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
And thou say in thy heart, My power and the strength of my hand have gotten me this wealth.
18 Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
But thou shalt remember the Lord thy God; for it is he that giveth thee power to get wealth; in order that he might fulfill his covenant which he hath sworn unto thy fathers, as it is this day.
19 In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
And it shall come to pass, that, if thou shouldst forget the Lord thy God, and walk after other gods, and serve them, and bow thyself down to them, I testify against you this day that ye shall surely perish;
20 Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.
Like the nations which the Lord destroyeth from before you, so shall ye perish; in recompense of that ye would not hearken unto the voice of the Lord your God.

< Maimaitawar Shari’a 8 >