< Maimaitawar Shari’a 7 >
1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku ƙasar da kuke shiga don ku mallaka, ya kuma kori al’ummai masu yawa a gabanku; wato, Hittiyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, al’ummai bakwai masu girma da ƙarfi fiye da ku.
When Yahweh your God brings you into the land that you go to possess, he will drive out many nations before you—the Hittites, the Girgashites, the Amorites, the Canaanites, the Perizzites, the Hivites, and the Jebusites—seven nations greater and mightier than you.
2 Sa’ad da kuma Ubangiji Allahnku ya ba da su gare ku, kuka kuma ci su da yaƙi, sai ku hallaka su ƙaƙaf. Kada ku yi yarjejjeniya da su, kada kuma ku nuna musu jinƙai.
It is Yahweh your God who gives them over to you when you defeat them, and then you must completely destroy them. You will make no covenant with them, and show them no mercy.
3 Kada ku yi auratayya da su. Kada ku ba da’ya’yanku mata wa’ya’yansu maza, ko ku ɗauko’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza.
Neither will you arrange any marriages with them. You will not give your daughters to their sons, and you will not take their daughters for your sons.
4 Gama za su juye’ya’yanku maza daga bina, su bauta waɗansu alloli, fushin Ubangiji kuma zai ƙuna a kanku da sauri, zai kuma hallaka ku.
For they will turn away your sons from following me, so that they may worship other gods. So the anger of Yahweh will be kindled against you, and he will destroy you quickly.
5 Ga abin da za ku yi da su, za ku rurrushe bagadansu, ku ragargaza keɓaɓɓun duwatsunsu, ku farfashe ginshiƙan Asheransu, ku kuma ƙona gumakansu da wuta.
This is how you will deal with them: You will break down their altars, dash their stone pillars in pieces, cut down their Asherah poles, and burn their cast idols.
6 Gama ku mutane masu tsarki ne ga Ubangiji Allahnku. Ubangiji Allahnku ya zaɓe ku daga dukan mutane a fuskar duniya, don ku zama mutanensa, kayan gādonsa.
For you are a nation that is set apart to Yahweh your God. He has chosen you to be a people for him to possess, more than all the other peoples that are on the face of the earth.
7 Ba don kun fi sauran al’ummai yawa ne ya sa Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma zaɓe ku ba, gama ku ne mafi ƙanƙanta cikin dukan al’ummai.
Yahweh did not set his love upon you or choose you because you were more in number than any people—for you were the fewest of all peoples—
8 Amma ya zama haka domin Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma kiyaye rantsuwar da ya yi wa kakanninku da ya fitar da ku da hannu mai ƙarfi, ya kuma cece ku daga ƙasar bauta, daga ikon Fir’auna sarkin Masar.
but because he loves you, and he wished to keep the oath that he had sworn to your fathers. This is why Yahweh has brought you out with a mighty hand and redeemed you out of the house of bondage, from the hand of Pharaoh, king of Egypt.
9 Saboda haka, ku sani cewa Ubangiji Allahnku, shi ne Allah; shi Allah ne mai aminci, yana kiyaye alkawarinsa na ƙauna ga tsararraki dubu na waɗanda suke ƙaunarsa suke kuma kiyaye umarnansa.
Therefore know that Yahweh your God—he is God, the faithful God, who keeps covenants and faithfulness for a thousand generations with those who love him and keep his commandments,
10 Amma waɗanda suke ƙinsa, a fili yakan sāka musu da hallaka; ba zai yi jinkiri yin ramuwa a kan maƙiyinsa ba, zai yi ramuwar a fili.
but repays those who hate him to their face, to destroy them; he will not be lenient on whoever hates him; he will repay him to his face.
11 Saboda haka, sai ku lura, ku bi umarnai, ƙa’idodi, da dokokin nan da nake ba ku a yau.
You will therefore keep the commandments, the statutes, and the decrees that I command you today, so that you will do them.
12 In kuka mai da hankali ga waɗannan dokoki, kuka kuma yi hankali ga bin su, to, Ubangiji Allahnku zai kiyaye alkawarinsa na ƙauna gare ku, kamar yadda ya rantse wa kakanninku.
If you listen to these decrees, and keep and do them, it will happen that Yahweh your God will keep with you the covenant and the faithfulness that he swore to your fathers.
13 Zai ƙaunace ku, yă albarkace ku, yă kuma ƙara yawanku. Zai albarkaci’ya’yanku, amfanin gonarku; hatsinku, sabon ruwan inabinku da kuma mai, ƙanana shanunku, da’yan tumaki na tumakinku, a ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku.
He will love you, bless you, and multiply you; he will also bless the fruit of your body and the fruit of your ground, your grain, your new wine, and your oil, the multiplication of your cattle and the young of your flocks, in the land that he swore to your fathers to give you.
14 Za a albarkace ku fiye da waɗansu mutane; babu wani cikin maza ko matanku da zai kasance babu haihuwa, ba kuwa wata dabbarku da za tă kasance babu haihuwa.
You will be blessed more than all other peoples; there will not be a childless male or a barren female among you or among your cattle.
15 Ubangiji zai kiyaye ku daga kowace cuta. Ba zai wahalshe ku da mugayen cututtukan da kuka sani a Masar ba, amma zai aukar wa dukan maƙiyanku.
Yahweh will take away from you all sickness; none of the evil diseases of Egypt that you have known will he put on you, but he will put them on all those who hate you.
16 Dole ku hallaka dukan mutanen da Ubangiji Allahnku ya bashe su gare ku. Kada ku ji tausayinsu, kada kuma ku bauta wa allolinsu, gama wannan zai zama tarko gare ku.
You will consume all the peoples whom Yahweh your God will give over to you, and your eye will not pity them. You will not worship their gods, for that will be a trap for you.
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Waɗannan al’ummai sun fi mu ƙarfi. Yaya za mu kore su?”
If you say in your heart, 'These nations are more numerous than I; how can I dispossess them?'—
18 Amma kada ku ji tsoronsu; ku tuna da kyau abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Fir’auna da kuma dukan Masar.
do not be afraid of them; you will call to mind what Yahweh your God did to Pharaoh and to all Egypt;
19 Kun ga da idanunku, manyan gwaje-gwaje, alamu masu banmamaki da al’ajabai, hannu mai ƙarfi da kuma mai ikon da Ubangiji Allahnku ya fitar da ku. Ubangiji Allahnku zai yi haka ga dukan mutanen da yanzu kuke tsoro.
the great sufferings that your eyes saw, the signs, the wonders, the mighty hand, and the outstretched arm by which Yahweh your God brought you out. Yahweh your God will do the same to all the peoples whom you fear.
20 Ban da haka ma, Ubangiji Allahnku zai aika da rina a cikinsu, har sai sun hallaka sauran mutanen da suka ragu, waɗanda suka ɓuya daga gare ku.
Moreover, Yahweh your God will send the hornet among them, until those who are left and who hide themselves from you perish from your presence.
21 Kada ku tsorata saboda su, gama Ubangiji Allahnku, wanda yake a cikinku, Allah ne mai girma da kuma mai banrazana.
You will not be frightened at them, for Yahweh your God is among you, a great and fearsome God.
22 Da kaɗan da kaɗan Ubangiji Allahnku zai kore waɗannan al’ummai a gabanku. Ba a bari ku hallaka su duka gaba ɗaya ba, in ba haka namun jeji za su yaɗu kewaye da ku.
Yahweh your God will drive out those nations before you little by little. You will not defeat them all at once, or the wild animals would become very many around you.
23 Amma Ubangiji Allahnku zai ba da su gare ku, yana jefa su cikin rikicewa mai girma, har sai an hallaka su.
But Yahweh your God will give you victory over them when you meet them in battle; he will greatly confuse them until they are destroyed.
24 Zai ba da sarakunsu a hannunku, za ku kuwa shafe sunayensu daga duniya. Babu wani da zai yi tsayayya da ku, za ku hallaka su.
He will put their kings under your power, and you will make their name perish from under heaven. No one will be able to stand before you, until you have destroyed them.
25 Ku ƙone siffar allolinsu da wuta. Kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariyar da aka rufe allolin da ita, Kada ku kwashe su, don kada su zamar muku tarko, gama abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku.
You will burn the carved figures of their gods—do not covet the silver or the gold that covers them and take it for yourself, because if you do, you will become trapped by it—for it is an abomination to Yahweh your God.
26 Kada ku kawo abin ƙyama cikin gidajenku, domin kada ku zama kamar su. Gaba ɗaya ku yi ƙyamarsu, ku ƙi su, gama an ware su, sun zama domin a hallaka.
You will not bring any abomination into your house and start to worship it. You will utterly detest and abhor it, for it is set apart for destruction.