< Maimaitawar Shari’a 7 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku ƙasar da kuke shiga don ku mallaka, ya kuma kori al’ummai masu yawa a gabanku; wato, Hittiyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, al’ummai bakwai masu girma da ƙarfi fiye da ku.
Ka Jehova Nyasaye ma Nyasachu okelou e piny ma udhi donjoe mondo ukaw obed maru, mi oriembonu ogendini mangʼeny kaka jo-Hiti, jo-Girgash, jo-Amor, jo-Kanaan, jo-Perizi, jo-Hivi kod jo-Jebus, ma gin pinje abiriyo madongo kendo maroteke moloyou.
2 Sa’ad da kuma Ubangiji Allahnku ya ba da su gare ku, kuka kuma ci su da yaƙi, sai ku hallaka su ƙaƙaf. Kada ku yi yarjejjeniya da su, kada kuma ku nuna musu jinƙai.
Kendo ka Jehova Nyasaye ma Nyasachu osechiwo gi e lwetu mi uloyogi, to une ni utiekogi duto. Kik ulos winjruok kodgi bende kik utimnegi ngʼwono.
3 Kada ku yi auratayya da su. Kada ku ba da’ya’yanku mata wa’ya’yansu maza, ko ku ɗauko’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza.
Kik ukendru kodgi. Kik uchiw nyiu ni yawuotgi kata kik yawuotu okend nyigi,
4 Gama za su juye’ya’yanku maza daga bina, su bauta waɗansu alloli, fushin Ubangiji kuma zai ƙuna a kanku da sauri, zai kuma hallaka ku.
nimar ginimi yawuotu weya mitine nyiseche mamoko kendo mano dimi mirima mak Jehova Nyasaye mitieku mapiyo nono.
5 Ga abin da za ku yi da su, za ku rurrushe bagadansu, ku ragargaza keɓaɓɓun duwatsunsu, ku farfashe ginshiƙan Asheransu, ku kuma ƙona gumakansu da wuta.
Ma e gima onego utimnegi: Mukuru kendegi mag misengini, touru kitegi mopa milamo, tongʼuru sirnigi mag Ashera kendo wangʼuru kido mag-gi milamo e mach.
6 Gama ku mutane masu tsarki ne ga Ubangiji Allahnku. Ubangiji Allahnku ya zaɓe ku daga dukan mutane a fuskar duniya, don ku zama mutanensa, kayan gādonsa.
Nimar un oganda mowal ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu. Jehova Nyasaye ma Nyasachu oseyierou kuom ogendini duto manie piny mondo ubed joge, joge owuon mogeno.
7 Ba don kun fi sauran al’ummai yawa ne ya sa Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma zaɓe ku ba, gama ku ne mafi ƙanƙanta cikin dukan al’ummai.
Jehova Nyasaye ne ok oherou mi oyierou nikech ne ungʼeny moloyo ogendini mamoko, nimar un e oganda matinie moloyo,
8 Amma ya zama haka domin Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma kiyaye rantsuwar da ya yi wa kakanninku da ya fitar da ku da hannu mai ƙarfi, ya kuma cece ku daga ƙasar bauta, daga ikon Fir’auna sarkin Masar.
to Jehova Nyasaye noyierou nikech noherou kendo orito singruok mane otimo gi kwereu kane ogolou gi tekone maduongʼ kendo warou e piny mane unie wasumbini, e lwet Farao ruodh Misri.
9 Saboda haka, ku sani cewa Ubangiji Allahnku, shi ne Allah; shi Allah ne mai aminci, yana kiyaye alkawarinsa na ƙauna ga tsararraki dubu na waɗanda suke ƙaunarsa suke kuma kiyaye umarnansa.
Ngʼeuru ni Jehova Nyasaye ma Nyasachu en Nyasaye. En Nyasaye ma ja-adiera; marito singruokne mar hera ne tienge gana gi gana mohere kendo rito chikene.
10 Amma waɗanda suke ƙinsa, a fili yakan sāka musu da hallaka; ba zai yi jinkiri yin ramuwa a kan maƙiyinsa ba, zai yi ramuwar a fili.
To jogo mochaye obiro kumo motiekgi mana ka gineno, adier ok obi deko ma ok okumo jogo mochaye.
11 Saboda haka, sai ku lura, ku bi umarnai, ƙa’idodi, da dokokin nan da nake ba ku a yau.
Kuom mano rituru yorene, buchene kod chikene adimba ma amiyou kawuono.
12 In kuka mai da hankali ga waɗannan dokoki, kuka kuma yi hankali ga bin su, to, Ubangiji Allahnku zai kiyaye alkawarinsa na ƙauna gare ku, kamar yadda ya rantse wa kakanninku.
Ka uchiko itu ne chikegi kendo uritogi adimba, eka Jehova Nyasaye ma Nyasachu norit singruokne mar hera kodu kaka ne osingore ne kwereu.
13 Zai ƙaunace ku, yă albarkace ku, yă kuma ƙara yawanku. Zai albarkaci’ya’yanku, amfanin gonarku; hatsinku, sabon ruwan inabinku da kuma mai, ƙanana shanunku, da’yan tumaki na tumakinku, a ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku.
Obiro herou, gwedhou kendo miyo unyaa mangʼeny, obiro gwedho nyithindo munywolo, cham manie puotheu, decheu, divai manyien, mo, nyiroye ma dhou onywolo kod nyithi jambu e piny mane osingore ne kwereu ni nomigi.
14 Za a albarkace ku fiye da waɗansu mutane; babu wani cikin maza ko matanku da zai kasance babu haihuwa, ba kuwa wata dabbarku da za tă kasance babu haihuwa.
Ibiro gwedhou moloyo ogendini duto; onge ngʼato kuomu madichwo kata madhako ma ok nobed maonge nyathi, kata jambu manobed maonge nyithindo.
15 Ubangiji zai kiyaye ku daga kowace cuta. Ba zai wahalshe ku da mugayen cututtukan da kuka sani a Masar ba, amma zai aukar wa dukan maƙiyanku.
Jehova Nyasaye notiek tuoche duto kuomu; bende ok nokelnu tuoche maricho mane uneno ka un Misri, to tuochego nomak mana wasiku mochayou.
16 Dole ku hallaka dukan mutanen da Ubangiji Allahnku ya bashe su gare ku. Kada ku ji tausayinsu, kada kuma ku bauta wa allolinsu, gama wannan zai zama tarko gare ku.
Nyaka utiek ji duto ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu keto e lwetu. Kik ukechgi bende kik ulam nyisechegi, nimar mano nobednu obadho.
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Waɗannan al’ummai sun fi mu ƙarfi. Yaya za mu kore su?”
Unyalo wacho kendu niya, “Ogendinigi tek moloyowa. Ere kaka wanyalo riembogi oko?”
18 Amma kada ku ji tsoronsu; ku tuna da kyau abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Fir’auna da kuma dukan Masar.
To kik uluorgi; paruru malongʼo gima ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu otimone Farao gi piny e Misri duto.
19 Kun ga da idanunku, manyan gwaje-gwaje, alamu masu banmamaki da al’ajabai, hannu mai ƙarfi da kuma mai ikon da Ubangiji Allahnku ya fitar da ku. Ubangiji Allahnku zai yi haka ga dukan mutanen da yanzu kuke tsoro.
Ne uneno kod wengeu tem malich, honni madongo tekone kod bat morie mane Jehova Nyasaye ma Nyasachu ogolougo oko. Jehova Nyasaye ma Nyasachu biro timo mano bende ne oganda makoro uluoro.
20 Ban da haka ma, Ubangiji Allahnku zai aika da rina a cikinsu, har sai sun hallaka sauran mutanen da suka ragu, waɗanda suka ɓuya daga gare ku.
To bende Jehova Nyasaye ma Nyasachu biro miyo kihondko omakgi ma kata ngʼato pond e dieru manade to ok notony.
21 Kada ku tsorata saboda su, gama Ubangiji Allahnku, wanda yake a cikinku, Allah ne mai girma da kuma mai banrazana.
Kik gimiu luoro nimar Jehova Nyasaye ma Nyasachu manie dieru duongʼ kendo en Nyasaye man-gi teko.
22 Da kaɗan da kaɗan Ubangiji Allahnku zai kore waɗannan al’ummai a gabanku. Ba a bari ku hallaka su duka gaba ɗaya ba, in ba haka namun jeji za su yaɗu kewaye da ku.
Jehova Nyasaye ma Nyasachu biro riembo ogendinigo kuomu matin tin mana ka uneno. Ok noyienu mondo utiekgi dichiel nimar dipo ka ondiegi onywolore mangʼeny mathagu.
23 Amma Ubangiji Allahnku zai ba da su gare ku, yana jefa su cikin rikicewa mai girma, har sai an hallaka su.
To Jehova Nyasaye ma Nyasachu nochiwgi e lwetu, kowito riekogi nyaka ginirum duto.
24 Zai ba da sarakunsu a hannunku, za ku kuwa shafe sunayensu daga duniya. Babu wani da zai yi tsayayya da ku, za ku hallaka su.
Obiro chiwo ruodhi mag ogendinigo e lwetu kendo unutiek nyingegi e bwo polo. Onge ngʼama nochungʼ masiru kendo unutiekgi duto.
25 Ku ƙone siffar allolinsu da wuta. Kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariyar da aka rufe allolin da ita, Kada ku kwashe su, don kada su zamar muku tarko, gama abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku.
Kido mag nyisechegi nyaka uwangʼ e mach. Kik ugomb fedha kod dhahabu ma gin-go, bende kik ukawgi. Ka utimo kamano, to ginibednu obadho nimar gigo gin gigo makwero ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu.
26 Kada ku kawo abin ƙyama cikin gidajenku, domin kada ku zama kamar su. Gaba ɗaya ku yi ƙyamarsu, ku ƙi su, gama an ware su, sun zama domin a hallaka.
Kik ukel gimoro makwero e uteu, nimar un kod gima ukelono nokethi. Kik ubed gi gik machalo kamano nimar enokethgi.

< Maimaitawar Shari’a 7 >