< Maimaitawar Shari’a 7 >
1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku ƙasar da kuke shiga don ku mallaka, ya kuma kori al’ummai masu yawa a gabanku; wato, Hittiyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, al’ummai bakwai masu girma da ƙarfi fiye da ku.
Naar Herren din Gud faar indført dig i Landet, som du skal komme hen til, at eje det, og faar udkastet mange Folk for dig, Hethiter og Girgasiter og Amoriter og Kananiter og Feresiter og Heviter og Jebusiter, syv Folk, som ere mangfoldigere og vældigere end du,
2 Sa’ad da kuma Ubangiji Allahnku ya ba da su gare ku, kuka kuma ci su da yaƙi, sai ku hallaka su ƙaƙaf. Kada ku yi yarjejjeniya da su, kada kuma ku nuna musu jinƙai.
og Herren din Gud har givet dem hen for dit Ansigt, og du har slaget dem: Da skal du bandlyse dem; du skal ikke gøre Pagt med dem og ej bevise dem Naade.
3 Kada ku yi auratayya da su. Kada ku ba da’ya’yanku mata wa’ya’yansu maza, ko ku ɗauko’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza.
Og du skal ikke gøre Svogerskab med dem; du skal ikke give hans Søn din Datter, og hans Datter skal du ikke tage til din Søn.
4 Gama za su juye’ya’yanku maza daga bina, su bauta waɗansu alloli, fushin Ubangiji kuma zai ƙuna a kanku da sauri, zai kuma hallaka ku.
Thi han skal bringe din Søn til at vige fra mig, og de skulle tjene andre Guder; og saa optændes Herrens Vrede imod eder, og han skal snart ødelægge eder.
5 Ga abin da za ku yi da su, za ku rurrushe bagadansu, ku ragargaza keɓaɓɓun duwatsunsu, ku farfashe ginshiƙan Asheransu, ku kuma ƙona gumakansu da wuta.
Men saaledes skulle I gøre ved dem: I skulle nedbryde deres Altere og sønderslaa deres Støtter og omhugge deres Astartebilleder og opbrænde deres udskaarne Billeder med Ild.
6 Gama ku mutane masu tsarki ne ga Ubangiji Allahnku. Ubangiji Allahnku ya zaɓe ku daga dukan mutane a fuskar duniya, don ku zama mutanensa, kayan gādonsa.
Thi du er et helligt Folk for Herren din Gud; Herren din Gud har udvalgt dig, at være ham til et Ejendoms Folk, fremfor alle Folk, som ere paa Jordens Kreds.
7 Ba don kun fi sauran al’ummai yawa ne ya sa Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma zaɓe ku ba, gama ku ne mafi ƙanƙanta cikin dukan al’ummai.
Herren har ikke haft Lyst til eder og udvalgt eder, fordi I vare mangfoldigere end alle Folk; thi I ere det mindste iblandt alle Folk.
8 Amma ya zama haka domin Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma kiyaye rantsuwar da ya yi wa kakanninku da ya fitar da ku da hannu mai ƙarfi, ya kuma cece ku daga ƙasar bauta, daga ikon Fir’auna sarkin Masar.
Men fordi Herren har elsket eder, og fordi han vilde holde den Ed, som han svor eders Fædre, har Herren udført eder med en stærk Haand, og han har frelst dig af Trælles Hus, af Faraos, Kongen af Ægyptens, Haand.
9 Saboda haka, ku sani cewa Ubangiji Allahnku, shi ne Allah; shi Allah ne mai aminci, yana kiyaye alkawarinsa na ƙauna ga tsararraki dubu na waɗanda suke ƙaunarsa suke kuma kiyaye umarnansa.
Saa skal du vide, at Herren din Gud, han er Gud, den trofaste Gud, som holder Pagten og Miskundheden mod dem, som elske ham, og mod dem, som holde hans Bud, til tusinde Led.
10 Amma waɗanda suke ƙinsa, a fili yakan sāka musu da hallaka; ba zai yi jinkiri yin ramuwa a kan maƙiyinsa ba, zai yi ramuwar a fili.
Og han betaler dem, som ham hade, øjensynligen, ved at lade dem omkomme; han skal ikke tøve med den, som hader ham, han skal betale ham øjensynligen.
11 Saboda haka, sai ku lura, ku bi umarnai, ƙa’idodi, da dokokin nan da nake ba ku a yau.
Saa hold det Bud og de Skikke og de Befalinger, som jeg byder dig i Dag, at du gør efter dem.
12 In kuka mai da hankali ga waɗannan dokoki, kuka kuma yi hankali ga bin su, to, Ubangiji Allahnku zai kiyaye alkawarinsa na ƙauna gare ku, kamar yadda ya rantse wa kakanninku.
Og det skal ske, fordi I høre disse Befalinger og holde dem og gøre dem, da skal og Herren din Gud holde dig den Pagt og den Miskundhed, som han har tilsvoret dine Fædre.
13 Zai ƙaunace ku, yă albarkace ku, yă kuma ƙara yawanku. Zai albarkaci’ya’yanku, amfanin gonarku; hatsinku, sabon ruwan inabinku da kuma mai, ƙanana shanunku, da’yan tumaki na tumakinku, a ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku.
Og han skal elske dig og velsigne dig og mangfoldiggøre dig, og han skal velsigne dit Livs Frugt og dit Lands Frugt, dit Korn og din nye Vin og din Olie, dine Øksnes Affødning og dit Smaakvægs megen Yngel i det Land, som han har tilsvoret dine Fædre at ville give dig.
14 Za a albarkace ku fiye da waɗansu mutane; babu wani cikin maza ko matanku da zai kasance babu haihuwa, ba kuwa wata dabbarku da za tă kasance babu haihuwa.
Du skal være velsignet fremfor alle Folk; der skal ingen ufrugtbar Han eller Hun være iblandt dig eller iblandt dit Kvæg.
15 Ubangiji zai kiyaye ku daga kowace cuta. Ba zai wahalshe ku da mugayen cututtukan da kuka sani a Masar ba, amma zai aukar wa dukan maƙiyanku.
Og Herren skal lade al Sygdom vige fra dig; og alle de ægyptiske slemme Sygdomme, som du kender, dem skal han ikke lægge paa dig, men lægge dem paa alle dem, som hade dig.
16 Dole ku hallaka dukan mutanen da Ubangiji Allahnku ya bashe su gare ku. Kada ku ji tausayinsu, kada kuma ku bauta wa allolinsu, gama wannan zai zama tarko gare ku.
Og du skal tilintetgøre alle de Folk, som Herren din Gud giver i din Vold, dit Øje skal ikke spare dem; og du skal ikke tjene deres Guder, thi det skal blive dig til en Snare.
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Waɗannan al’ummai sun fi mu ƙarfi. Yaya za mu kore su?”
Naar du siger i dit Hjerte: Disse Folk ere mangfoldigere end jeg, hvorledes formaar jeg at fordrive dem?
18 Amma kada ku ji tsoronsu; ku tuna da kyau abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Fir’auna da kuma dukan Masar.
da skal du ikke frygte for dem; du skal komme i Hu, hvad Herren din Gud gjorde ved Farao og ved alle Ægypterne,
19 Kun ga da idanunku, manyan gwaje-gwaje, alamu masu banmamaki da al’ajabai, hannu mai ƙarfi da kuma mai ikon da Ubangiji Allahnku ya fitar da ku. Ubangiji Allahnku zai yi haka ga dukan mutanen da yanzu kuke tsoro.
de store Forsøgelser, som dine Øjne saa, og de Tegn og de underlige Ting og den stærke Haand og den udrakte Arm, ved hvilken Herren din Gud udførte dig; saaledes skal Herren din Gud gøre imod alle de Folk, for hvis Ansigt du frygter.
20 Ban da haka ma, Ubangiji Allahnku zai aika da rina a cikinsu, har sai sun hallaka sauran mutanen da suka ragu, waɗanda suka ɓuya daga gare ku.
Og Herren din Gud skal endog sende Gedehamser paa dem, indtil de omkomme, som ere blevne tilovers, og som have skjult sig for dit Ansigt.
21 Kada ku tsorata saboda su, gama Ubangiji Allahnku, wanda yake a cikinku, Allah ne mai girma da kuma mai banrazana.
Du skal ikke forfærdes for deres Ansigt; thi Herren din Gud er midt iblandt dig, en stor og forfærdelig Gud.
22 Da kaɗan da kaɗan Ubangiji Allahnku zai kore waɗannan al’ummai a gabanku. Ba a bari ku hallaka su duka gaba ɗaya ba, in ba haka namun jeji za su yaɗu kewaye da ku.
Og Herren din Gud skal efterhaanden uddrive disse Folk for dit Ansigt; du kan ikke saa snart gøre Ende paa dem, for at de vilde Dyr paa Marken ikke skulle blive mange imod dig.
23 Amma Ubangiji Allahnku zai ba da su gare ku, yana jefa su cikin rikicewa mai girma, har sai an hallaka su.
Og Herren din Gud skal give dem hen for dit Ansigt og forstyrre dem med en stor Forstyrrelse, indtil de ødelægges.
24 Zai ba da sarakunsu a hannunku, za ku kuwa shafe sunayensu daga duniya. Babu wani da zai yi tsayayya da ku, za ku hallaka su.
Og han skal give deres Konger i din Haand, og du skal udslette deres Navn fra at være under Himmelen; der skal ingen kunne staa imod dit Ansigt, indtil du har ødelagt dem.
25 Ku ƙone siffar allolinsu da wuta. Kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariyar da aka rufe allolin da ita, Kada ku kwashe su, don kada su zamar muku tarko, gama abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku.
I skulle opbrænde deres Guders udskaarne Billeder med Ild; du skal ikke begære Sølvet eller Guldet, som er paa dem, eller tage det til dig, at du ikke besnæres dermed; thi det er Herren din Gud en Vederstyggelighed.
26 Kada ku kawo abin ƙyama cikin gidajenku, domin kada ku zama kamar su. Gaba ɗaya ku yi ƙyamarsu, ku ƙi su, gama an ware su, sun zama domin a hallaka.
Og du skal ikke lade Vederstyggelighed komme i dit Hus, at du ikke skal blive en forbandet Ting, ligesom dette er; du skal helt væmmes med Væmmelse derfor og have stor Vederstyggelighed for det, thi det er en forbandet Ting.