< Maimaitawar Shari’a 6 >
1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
Desse äro nu de lag, och bud, och rätter, som Herren edar Gud budit hafver, att I dem lära och göra skolen i landena, dit I indragen till att intaga det;
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
Att du fruktar Herran din Gud, och håller alla hans rätter och bud, som jag bjuder dig; du och din barn, och din barnabarn, i alla edra lifsdagar, på det I skolen länge lefva.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Israel, du skall höra, och behållat, så att du gör ock så, att dig väl går, och varder mycket förökad, såsom Herren dina fäders Gud dig tillsagt hafver ett land, der mjölk och hannog uti flyter.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Hör, Israel: Herren vår Gud är en enig Herre.
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
Och du skall älska Herran din Gud af allo hjerta, af allo själ, af allo förmågo.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
Och dessa ord, som jag bjuder dig i dag, skall du lägga på hjertat;
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
Och skall skärpa dem dinom barnom, och derom tala, när du sitter i ditt hus, eller går uppå vägen; när du nederlägger dig, eller uppstår;
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
Och skall binda dem för ett tecken på dine hand, och skola vara dig till en åminnelse för din ögon;
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
Och skall skrifva dem på dins hus dörrträ, och uppå dörrena.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
När nu Herren din Gud låter dig komma uti landet, som han dina fäder, Abraham, Isaac och Jacob, svorit hafver, dig att gifva stora och sköna städer, som du intet byggt hafver;
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
Och hus full med allt godt, de du intet uppfyllt hafver; och uthuggna brunnar, som du intet uthuggit hafver; och vingårdar och oljoberg, som du intet planterat hafver, att du må äta och mätt varda;
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
Så tag dig vara, att du icke förgäter Herran, som dig utur Egypti land, utu träldomens hus, fört hafver;
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
Utan skall frukta Herran din Gud, och tjena honom, och svärja vid hans Namn;
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
Och skall icke följa andra gudar efter, dess folks, som omkring eder bo;
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
Ty Herren din Gud är en nitälskande Gud ibland dig; att Herrans dins Guds vrede icke skall förgrymma sig öfver dig, och förgöra dig af jordene.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
I skolen icke försöka Herran edar Gud, såsom I försökten honom i Massa;
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
Utan skolen hålla Herrans edars Guds bud, och hans vittnesbörder, och hans rätter, som han budit hafver;
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
Att du gör det rätt och godt är för Herrans ögon, på det dig må gå väl, och du inkommer, och intager det goda landet, som Herren svorit hafver dina fäder;
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
Att han skall fördrifva alla dina fiendar för dig, såsom Herren sagt hafver.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
När nu din son i dag eller i morgon frågar dig, och säger: Hvad är detta för vittnesbörder, bud och rätter, som Herren vår Gud eder budit hafver?
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
Så skall du säga dinom son: Vi vorom Pharaos trälar i Egypten; och Herren förde oss utur Egypten med mägtiga hand.
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
Och Herren gjorde stor och ond tecken och under öfver Egypten och Pharao, och allt hans hus, för vår ögon;
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
Och förde oss dädan, på det han skulle införa oss, och gifva oss det land, som han våra fäder svorit hade.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
Och böd Herren oss att göra efter alla dessa rätter, att vi skole frukta Herran vår Gud, att oss väl går i alla våra lifsdagar, såsom det tillgår i denna dag.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
Och det skall vara oss till rättfärdighet för Herranom vårom Gud, om vi hålle och göre all dessa buden, såsom han oss budit hafver.