< Maimaitawar Shari’a 6 >

1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
Lale yimilayo, izimiso, lezahlulelo iNkosi uNkulunkulu wenu elaya ukulifundisa, ukuthi lizenze elizweni elichaphela kulo ukuthi lidle ilifa lalo,
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
ukuze uyesabe iNkosi uNkulunkulu wakho, ukugcina zonke izimiso zayo lemithetho yayo engikulaya yona, wena lendodana yakho lendodana yendodana yakho, zonke izinsuku zempilo yakho, ukuze insuku zakho zelulwe.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Ngakho zwana, Israyeli, unanzelele ukuzenza, ukuze kukulungele, ukuze wande kakhulu, njengokuthembisa kweNkosi uNkulunkulu waboyihlo kuwe, elizweni eligeleza uchago loluju.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Zwana, Israyeli, iNkosi uNkulunkulu wethu, yiNkosi yinye.
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
Njalo wothanda iNkosi uNkulunkulu wakho ngenhliziyo yakho yonke langomphefumulo wakho wonke langamandla akho wonke.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
Njalo amazwi la engikulaya ngawo lamuhla azakuba senhliziyweni yakho;
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
njalo uzawafundisa abantwana bakho ngokukhuthala, uzakhuluma ngawo lapho uhlezi endlini yakho, lalapho uhamba endleleni, lalapho ulala, lalapho uvuka.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
Uzawabophela esandleni sakho abe luphawu, njalo abe ngamafilakteriyu phakathi laphakathi kwamehlo akho.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
Njalo uzawabhala emigubazini yendlu yakho, lemasangweni akho.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
Kuzakuthi lapho iNkosi uNkulunkulu wakho ikungenisa elizweni eyafunga kuboyihlo, kuAbrahama, kuIsaka lakuJakobe, ukukunika imizi emikhulu lemihle, ongayakhanga,
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
lezindlu ezigcwele zonke izinto ezinhle, ongazigcwalisanga, lemithombo eyagejwayo ongayigebhanga, izivini lezihlahla zemihlwathi ongazihlanyelanga, lapho udlile wasutha,
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
ziqaphele, hlezi uyikhohlwe iNkosi eyakukhupha elizweni leGibhithe, endlini yobugqili.
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
Uzayesaba iNkosi uNkulunkulu wakho, uyikhonze, ufunge ngebizo layo.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
Lingalandeli abanye onkulunkulu, babonkulunkulu bezizwe ezilizungelezeleyo.
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
Ngoba iNkosi uNkulunkulu wakho inguNkulunkulu olobukhwele phakathi kwakho, hlezi ulaka lweNkosi uNkulunkulu wakho lukuvuthele, ikuchithe usuke ebusweni bomhlaba.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
Lingayilingi iNkosi uNkulunkulu wenu njengalokhu layilinga eMasa.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
Ligcine lokugcina imilayo yeNkosi uNkulunkulu wenu, lobufakazi bayo, lezimiso zayo, ekulaye zona.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
Njalo wenze okuqondileyo lokulungileyo emehlweni eNkosi, ukuze kukulungele, lokuthi ungene udle ilifa lelizwe elihle, iNkosi eyalifungela oyihlo,
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
ukuxotsha zonke izitha zakho phambi kwakho, njengalokhu iNkosi ikhulumile.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
Lapho indodana yakho ikubuza esikhathini esizayo isithi: Buyini ubufakazi lezimiso lezahlulelo iNkosi uNkulunkulu wethu elilaye zona?
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
Khona uzakuthi endodaneni yakho: Sasiyizigqili zikaFaro eGibhithe, leNkosi yasikhupha eGibhithe ngesandla esilamandla.
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
Njalo iNkosi yenza izibonakaliso lezimangaliso ezinkulu lezimbi eGibhithe, phezu kukaFaro laphezu kwendlu yakhe yonke, phambi kwamehlo ethu.
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
Yasikhupha khona ukuze isingenise, ukusinika ilizwe eyalifungela obaba.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
INkosi yasisilaya ukwenza zonke lezizimiso, ukwesaba iNkosi uNkulunkulu wethu, ukuze kusilungele insuku zonke, ukusilondoloza siphila njengalamuhla.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
Kuzakuba yikulunga kithi, uba sinanzelela ukwenza limilayo yonke phambi kweNkosi uNkulunkulu wethu, njengokusilaya kwayo.

< Maimaitawar Shari’a 6 >