< Maimaitawar Shari’a 6 >
1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
And this is the commandment, with the statutes, and the ordinances, which the Lord your God hath commanded to teach you, to do them in the land whither ye are passing over to possess it:
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
In order that you mayest fear the Lord thy God, to keep all his statutes and his commandments, which I command thee, thou and thy son, and thy son's son, all the days of thy life; and in order that thy days may be prolonged.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Hear, therefore, O Israel, and observe to do them; that it may be well with thee, and that ye may increase greatly, as the Lord the God of thy fathers hath spoken to thee, [in] the land flowing with milk and honey.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Hear, O Israel! The Lord, our God, is the One Eternal Being.
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
And thou shalt love the Lord thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thy might.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
And these words which I command thee this day, shall be in thy heart:
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
And thou shalt teach them diligently unto thy children, and thou shalt speak of them when thou sittest in thy house, and when thou walkest by the way, and when thou liest down, and when thou risest up.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
And thou shalt bind them for a sign upon thy hand, and they shall be as frontlets between thy eyes.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
And thou shalt write them upon the door-posts of thy house, and upon thy gates.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
And it shall be, when the Lord thy God shall bring thee into the land which he hath sworn unto thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give unto thee, great and goodly cities, which thou didst not build,
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
And houses full of all good things, which thou didst not fill, and wells hewed out which thou didst not hew, vineyards and olive-trees, which thou didst not plant; and thou hast eaten and art satisfied:
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
Then beware that thou do not forget the Lord, who hath brought thee forth out of the land of Egypt, from the house of slavery.
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
The Lord thy God shalt thou fear, and him shalt thou serve, and by his name shalt thou swear.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
Ye shall not go after other gods, of the gods of the nations which are round about you;
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
For the Lord thy God is a watchful God among you: so that the anger of the Lord thy God may not be kindled against thee, and he destroy thee from off the face of the earth.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
Ye shall not tempt the Lord your God, as ye tempted him in Massah.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
Ye shall diligently keep the commandments of the Lord your God, and his testimonies, and his statutes, which he hath commanded thee.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
And thou shalt do that which is right and good in the eyes of the Lord; in order that it may be well with thee, and that thou mayest go in and take possession of the good land which the Lord hath sworn unto thy fathers,
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
To cast out all thy enemies from before thee; as the Lord hath spoken.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
When thy son should ask thee in time to come, saying, What mean the testimonies, and the statutes, and the ordinances, which the Lord our God hath commanded you?
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
Then shalt thou say unto thy son, We were bondmen unto Pharaoh in Egypt; and the Lord brought us out of Egypt with a mighty hand;
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
And the Lord let come signs and wonders, great and sore, on Egypt, on Pharaoh, and on all his household, before our eyes;
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
And us he brought out from there; in order to bring us in, to give us the land which he had sworn unto our fathers.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
And the Lord commanded us to do all these statutes, to fear the Lord our God; that it might be well with us at all times, and that he might preserve us alive, as it is at this day.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
And it shall be accounted righteousness unto us, if we observe to do all this commandment before the Lord our God, as he hath commanded us.