< Maimaitawar Shari’a 6 >

1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
Now these are the commandments, the statutes, and the judgments, which the LORD your God commanded to teach you, that all of you might do them in the land where all of you go to possess it:
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
That you might fear the LORD your God, to keep all his statutes and his commandments, which I command you, you, and your son, and your son's son, all the days of your life; and that your days may be prolonged.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Hear therefore, O Israel, and observe to do it; that it may be well with you, and that all of you may increase mightily, as the LORD God of your fathers has promised you, in the land that flows with milk and honey.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Hear, O Israel: The LORD our God is one LORD:
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
And you shall love the LORD your God with all of your heart, and with all your soul, and with all your might.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
And these words, which I command you this day, shall be in your heart:
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
And you shall teach them diligently unto your children, and shall talk of them when you sit in your house, and when you walk by the way, and when you lie down, and when you rise up.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
And you shall bind them for a sign upon your hand, and they shall be as frontlets between your eyes.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
And you shall write them upon the posts of your house, and on your gates.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
And it shall be, when the LORD your God shall have brought you into the land which he swore unto your fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give you great and goodly cities, which you builded not,
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
And houses full of all good things, which you filled not, and wells dug, which you dug not, vineyards and olive trees, which you planted not; when you shall have eaten and be full;
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
Then beware lest you forget the LORD, which brought you forth out of the land of Egypt, from the house of bondage.
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
You shall fear the LORD your God, and serve him, and shall swear by his name.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
All of you shall not go after other gods, of the gods of the people which are round about you;
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
(For the LORD your God is a jealous God among you) lest the anger of the LORD your God be kindled against you, and destroy you from off the face of the earth.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
All of you shall not tempt the LORD your God, as all of you tempted him in Massah.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
All of you shall diligently keep the commandments of the LORD your God, and his testimonies, and his statutes, which he has commanded you.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
And you shall do that which is right and good in the sight of the LORD: that it may be well with you, and that you may go in and possess the good land which the LORD swore unto your fathers.
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
To cast out all of your enemies from before you, as the LORD has spoken.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
And when your son asks you in time to come, saying, What mean the testimonies, and the statutes, and the judgments, which the LORD our God has commanded you?
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
Then you shall say unto your son, We were Pharaoh's bondmen in Egypt; and the LORD brought us out of Egypt with a mighty hand:
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
And the LORD showed signs and wonders, great and sore, upon Egypt, upon Pharaoh, and upon all his household, before our eyes:
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
And he brought us out from thence, that he might bring us in, to give us the land which he swore unto our fathers.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
And the LORD commanded us to do all these statutes, to fear the LORD our God, for our good always, that he might preserve us alive, as it is at this day.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
And it shall be our righteousness, if we observe to do all these commandments before the LORD our God, as he has commanded us.

< Maimaitawar Shari’a 6 >