< Maimaitawar Shari’a 6 >

1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
“These are the precepts and ceremonies, as well as the judgments, which the Lord your God has commanded that I teach to you, which you shall do in the land to which you will travel in order to possess it.
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
So may you fear the Lord your God, and keep all his commandments and precepts, which I am entrusting to you, and to your sons and grandsons, all the days of your life, so that your days may be prolonged.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Listen and observe, O Israel, so that you may do just as the Lord has instructed you, and it may be well with you, and you may be multiplied all the more, for the Lord, the God of your fathers, has promised you a land flowing with milk and honey.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Listen, O Israel: the Lord our God is one Lord.
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
You shall love the Lord your God with all your heart, and with all your soul, and with all your strength.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
And these words, which I instruct to you this day, shall be in your heart.
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
And you shall explain them to your sons. And you shall meditate upon them sitting in your house, and walking on a journey, when lying down and when rising up.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
And you shall bind them like a sign on your hand, and they shall be placed and shall move between your eyes.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
And you shall write them at the threshold and on the doors of your house.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
And when the Lord your God will have led you into the land, about which he swore to your fathers, Abraham, Isaac, and Jacob, and when he will have given to you great and excellent cities, which you did not build;
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
houses full of goods, which you did not amass; cisterns, which you did not dig; vineyards and olive groves, which you did not plant;
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
and when you will have eaten and been satisfied:
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
take care diligently, lest you forget the Lord, who led you away from the land of Egypt, from the house of servitude. You shall fear the Lord your God, and you shall serve him alone, and you shall swear by his name.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
You shall not go after the strange gods of all the Gentiles, who are around you.
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
For the Lord your God is a jealous God in your midst. Otherwise, at some time, the fury of the Lord your God may be enraged against you, and he may take you away from the face of the earth.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
You shall not tempt the Lord your God, as you tempted him in the place of temptation.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
Keep the precepts of the Lord your God, as well as the testimonies and ceremonies, which he has instructed to you.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
And do what is pleasing and good in the sight of the Lord, so that it may be well with you, and so that, when you enter, you may possess the excellent land, about which the Lord swore to your fathers
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
that he would wipe away all your enemies before you, just as he has spoken.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
And when your son will ask you tomorrow, saying: ‘What do these testimonies and ceremonies and judgments mean, which the Lord our God has entrusted to us?’
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
You shall say to him: ‘We were servants of Pharaoh in Egypt, and the Lord led us away from Egypt with a strong hand.
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
And he wrought signs and wonders, great and very grievous, in Egypt, against Pharaoh and all his house, in our sight.
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
And he led us away from that place, so that he might lead us in and give us the land, about which he swore to our fathers.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
And the Lord instructed us that we should do all these ordinances, and that we should fear the Lord our God, so that it may be well with us all the days of our life, just as it is today.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
And he will be merciful to us, if we keep and perform all his precepts, in the sight of the Lord our God, just as he has commanded us.’”

< Maimaitawar Shari’a 6 >