< Maimaitawar Shari’a 6 >

1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
Now this is the commandment, the statutes and the ordinances, which Jehovah your God commanded to teach you, that ye might do them in the land where ye go over to possess it,
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
that thou might fear Jehovah thy God, to keep all his statutes and his commandments, which I command thee, thou, and thy son, and thy son's son, all the days of thy life, and that thy days may be prolonged.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Hear therefore, O Israel, and observe to do it, that it may be well with thee, and that ye may increase mightily, as Jehovah, the God of thy fathers, has promised to thee, in a land flowing with milk and honey.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Hear, O Israel: Jehovah our God is one Jehovah.
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
And thou shall love Jehovah thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thy might.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
And these words, which I command thee this day, shall be upon thy heart.
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
And thou shall teach them diligently to thy sons, and shall talk of them when thou sit in thy house, and when thou walk by the way, and when thou lie down, and when thou rise up.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
And thou shall bind them for a sign upon thy hand, and they shall be for frontlets between thine eyes.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
And thou shall write them upon the door-posts of thy house, and upon thy gates.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
And it shall be, when Jehovah thy God shall bring thee into the land which he swore to thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give thee, great and goodly cities, which thou did not build,
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
and houses full of all good things, which thou did not fill, and cisterns hewn out, which thou did not hew, vineyards and olive trees, which thou did not plant, and thou shall eat and be full,
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
then beware lest thou forget Jehovah, who brought thee forth out of the land of Egypt, out of the house of bondage.
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
Thou shall fear Jehovah thy God, and him thou shall serve, and shall swear by his name.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
Ye shall not go after other gods, of the gods of the peoples that are round about you,
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
for Jehovah thy God in the midst of thee is a jealous God, lest the anger of Jehovah thy God be kindled against thee, and he destroy thee from off the face of the earth.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
Ye shall not challenge Jehovah your God, as ye challenged him in Massah.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
Ye shall diligently keep the commandments of Jehovah your God, and his testimonies, and his statutes, which he has commanded thee.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
And thou shall do that which is right and good in the sight of Jehovah, that it may be well with thee, and that thou may go in and possess the good land which Jehovah swore to thy fathers,
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
to thrust out all thine enemies from before thee, as Jehovah has spoken.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
When thy son asks thee in time to come, saying, What is the meaning of the testimonies, and the statutes, and the ordinances, which Jehovah our God has commanded you?
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
Then thou shall say to thy son, We were Pharaoh's bondmen in Egypt, and Jehovah brought us out of Egypt with a mighty hand.
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
And Jehovah showed signs and wonders, great and grievous, upon Egypt, upon Pharaoh, and upon all his house, before our eyes.
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
And he brought us out from there that he might bring us in to give us the land which he swore to our fathers.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
And Jehovah commanded us to do all these statutes, to fear Jehovah our God for our good always, that he might preserve us alive as at this day.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
And it shall be righteousness to us, if we observe to do all this commandment before Jehovah our God as he has commanded us.

< Maimaitawar Shari’a 6 >