< Maimaitawar Shari’a 6 >

1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
Tahae kah olpaek, oltlueh neh laitloeknah he pang ham na muk uh khohmuen ah nangmih cang puei ham neh saii sak ham ni na BOEIPA Pathen loh n'uen.
2 saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
Te dongah na BOEIPA Pathen te na rhih tih a khosing neh a olpaek boeih te namah neh na ca long khaw, na ca kah a ca long khaw, na hing tue khuiah ngaithuen sak ham ni kai loh nang kang uen. Te daengah ni na hinglung a vang eh.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
Aw Israel na yaak van coeng dongah na ngai ham te ngaithuen lah. Te long ni nang te khophoeng m'pha sak vetih na pa rhoek kah BOEIPA Pathen loh nang taengah a thui vanbangla suktui neh khoitui aka long khohmuen ah muep na ping eh.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Israel aw hnatun lah BOEIPA pakhat bueng ni mamih kah BOEIPA Pathen la aka om.
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
Na BOEIPA Pathen te na thinko boeih, na hinglu boeih, na cungkuem boeih neh lungnah lah.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
Tihnin ah kai loh nang kang uen olka he nang kah thinko ah rhaehrhong lah saeh.
7 Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
Na ca rhoek pum dongah pak pah lamtah na im ah na ngol vaengah khaw, long na caeh vaengah khaw, na yalh vaengah khaw, na thoh vaengah khaw thui pah.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
Na kut ah miknoek la cin pah lamtah na mikhmuh ah samtoelrhui bangla om saeh.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
Na im rhungsut neh na vongka dongah khaw daek pah.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
Tedae nang taengah paek ham na pa rhoek Abraham, Isaak neh Jakob taengah a caeng tangtae na thoong mueh khopuei dangka neh aka then,
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
Na sang pawt dae thennah cungkuem neh aka khawk im la, na vuet pawt dae a vueh tangtae tuito la, misur neh olive khaw na tue pawt dae na caak tih na hah nah khohmuen ah nang aka thak la na BOEIPA Pathen te om bitni.
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
Namah te ngaithuen, Egypt kho lamkah sal imkhui lamloh nang aka khuen BOEIPA te na hnilh ve.
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
Na BOEIPA Pathen te rhih lah. Amah taengah tho na thueng phoeiah ni a ming nen khaw na toemngam eh.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
Na kaepvai pilnam rhoek kah pathen, hlangtloe pathen hnukah cet boeh.
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
Na khui kah na Pathen BOEIPA tah thatlai Pathen ni. Na BOEIPA Pathen kah a thintoek he nang taengah ha sai vetih nang te diklai maelhmai dong lamloh m'mit sak ve.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
Massah ah na noemcai uh bangla na BOEIPA Pathen te noemcai uh boeh.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
Na BOEIPA Pathen kah olpaek khaw, a olphong neh a oltlueh nang n'uen te khaw ngaithuen rhoela ngaithuen.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
BOEIPA mikhmuh ah a thuem neh a then la saii. Te daengah ni nang te khophoeng m'pha sak phoeiah na pa rhoek taengah BOEIPA loh a caeng khohmuen then te na paan vetih na pang eh.
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
BOEIPA loh a thui vanbangla na thunkha boeih te na mikhmuh lamloh a thaek ni.
20 Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
Thangvuen ah na ca loh nang n'dawt tih, 'Mamih BOEIPA Pathen kah olphong, oltlueh neh laitloeknah te balae,’ a ti ni.
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
Na ca taengah, “Egypt ah Pharaoh sal la n'om uh vaengah BOEIPA loh tlungluen kut neh Egypt lamkah mamih n'doek.
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
BOEIPA loh mamih mikhmuh ah Egypt soah, Pharaoh neh a imkhui boeih soah miknoek neh kopoekrhai a len koek neh yoethae te a paek.
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
Tedae mamih tah a pa rhoek taengah a caeng sut khohmuen te mamih taengah paek ham ni te lamloh n'loh tih n'khuen.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
Tihnin kah bangla mamih aka hing sak ham mamih ham khohnin takuem a then dongah mamih kah BOEIPA Pathen rhih ham neh he rhoek kah oltlueh boeih he vai sak ham BOEIPA loh mamih n'uen coeng.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
Mamih n'uen vanbangla tahae kah olpaek boeih he mamih kah BOEIPA Pathen mikhmuh ah vai ham n'ngaithuen uh atah mamih ham duengnah la om van ni.

< Maimaitawar Shari’a 6 >