< Maimaitawar Shari’a 5 >
1 Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
And he summoned Moses all Israel and he said to them hear O Israel the statutes and the judgments which I [am] speaking in ears your this day and you will learn them and you will take care to observe them.
2 Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
Yahweh God our he made with us a covenant at Horeb.
3 Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
Not with ancestors our he made Yahweh the covenant this for with us we these here this day all of us alive.
4 Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
Face - on face he spoke Yahweh with you at the mountain from [the] middle of the fire.
5 (A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
I [was] standing between Yahweh and between you at the time that to declare to you [the] word of Yahweh for you were afraid of the fire and not you went up on the mountain saying.
6 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
I [am] Yahweh God your who I brought out you from [the] land of Egypt (from a house of slaves. *L(p)*)
7 “Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
(Not it will belong to you gods other *L(p)*) on (face my. *L(p)*)
8 Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
(Not you must make for yourself an image of - *L(p)*) any (form which [is] in the heavens - above and which [is] on the earth beneath *L(p)*) and which ([is] in the waters - from under to the earth. *L(p)*)
9 Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
Not (you must bow down to them *L(p)*) and not (you must be enticed to serve them *L(p)*) for I Yahweh God your [am] a God jealous [who] visits [the] iniquity of parents on children and on a third generation and on a fourth generation (of [those who] hate me. *L(p)*)
10 Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
(And [who] does covenant loyalty *L(p)*) (to thousands *L(b+p)*) of [those who] love me and of [those who] keep (commandments my. *Q(K)*)
11 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
Not you must take [the] name of Yahweh God your for emptiness for not he will leave unpunished Yahweh [one] who he will take name his for emptiness.
12 Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
(Keep *L(p)*) ([the] day of the sabbath to set apart as holy it *L(p)*) just as (he commanded you - Yahweh God your. *L(p)*)
13 Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
(Six days *L(p)*) (you will labor *L(b+p)*) (and you will do all work your. *L(p)*)
14 amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
And [the] day (seventh [is] a sabbath - *L(p)*) (to Yahweh *L(b+p)*) (God your *L(p)*) not you must do any work you and son your and daughter your and [male] servant your and female servant your and ox your and donkey your and all livestock your and sojourner your who [is] in gates your so that he may rest [male] servant your and female servant your (like you. *L(p)*)
15 Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
(And you will remember *L(p)*) that (a slave you were - *L(p)*) in [the] land of (Egypt and he brought out you Yahweh God your from there by a hand strong *L(p)*) and by an arm (outstretched *L(p)*) there-fore he has commanded you Yahweh God your to observe [the] day of the sabbath.
16 Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Honor father your and mother your just as he has commanded you Yahweh God your so that - they may be long! days your and so that it may go well for you on the land which Yahweh God your [is] about to give to you.
(Not you must murder. *L(p)*)
(And not you must commit adultery. *L(p)*)
(And not you must steal. *L(p)*)
20 Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
And not you must testify against neighbor your testimony of falsehood.
21 Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
And not you must covet [the] wife of neighbor your. And not you must desire [the] house of neighbor your field his and [male] servant his and female servant his ox his and donkey his and all that [belongs] to neighbor your.
22 Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
The words these he spoke Yahweh to all assembly your at the mountain from [the] middle of the fire the cloud and the thick darkness a voice great and not he added and he inscribed them on two tablets of stone and he gave them to me.
23 Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
And it was when heard you the voice from [the] middle of the darkness and the mountain [was] burning with fire and you drew near! to me all [the] chiefs of tribes your and elders your.
24 Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
And you said here! he has shown us Yahweh God our glory his and greatness his and voice his we have heard from [the] middle of the fire the day this we have seen that he speaks God with humankind and he will live.
25 Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
And therefore why? will we die for it will consume us the fire great this if [are] repeating - we to hear [the] voice of Yahweh God our again and we will die.
26 Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
For who? [is] all flesh who he has heard [the] voice of God living speaking from [the] middle of the fire like us and he has lived.
27 Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
Draw near you and hear all that he will say Yahweh God our and you - you will speak to us all that he will speak Yahweh God our to you and we will listen and we will do [it].
28 Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
And he heard Yahweh [the] sound of words your when spoke you to me and he said Yahweh to me I have heard [the] sound of [the] words of the people this which they spoke to you they have done well all that they have spoken.
29 Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
Who? will he give and it will belong heart their this to them to fear me and to keep all commandments my all the days so that it may go well for them and for children their for ever.
30 “Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
Go say to them return yourselves to tents your.
31 Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
And you here stand with me so let me speak to you all the commandment and the statutes and the judgments which you will teach them and they will observe [them] in the land which I [am] about to give to them to take possession of it.
32 Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
And you will take care to do just as he has commanded Yahweh God your you not you must turn aside right [hand] and left [hand].
33 Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.
In all the way which he has commanded Yahweh God your you you will walk so that you may live! and it will be good for you and you will prolong days in the land which you will take possession of!