< Maimaitawar Shari’a 4 >

1 To, ku ji, ya Isra’ila, ku kasa kunne ga ƙa’idodi da dokokin da nake shirin koya muku. Ku bi su domin ku yi tsawon rai, ku kuma shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku yake ba ku.
اکنون ای اسرائیل، به قوانینی که به شما یاد می‌دهم به دقت گوش کنید و اگر می‌خواهید زنده مانده، به سرزمینی که خداوند، خدای پدرانتان به شما داده است داخل شوید و آن را تصاحب کنید از این دستورها اطاعت نمایید.
2 Kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin abin da nake umarce ku. Amma ku kiyaye umarnan nan na Ubangiji Allahnku, da na ba ku.
قوانین دیگری به اینها نیفزایید و چیزی کم نکنید، بلکه فقط این دستورها را اجرا کنید؛ زیرا این قوانین از جانب خداوند، خدایتان می‌باشد.
3 Da idanunku, kun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba’al-Feyor. Yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka waɗansu daga cikinku waɗanda suka yi wa Ba’al-Feyor sujada,
دیدید که چگونه یهوه خدایتان در بعل فغور همهٔ کسانی را که بت بعل را پرستیدند از بین برد،
4 Amma ku da kuka manne ga Ubangiji Allahnku, kuna da rai har wa yau.
ولی همگی شما که به خداوند، خدایتان وفادار بودید تا به امروز زنده مانده‌اید.
5 Ga shi, na koya muku ƙa’idodi da dokoki, yadda Ubangiji Allahna ya umarce ni, don ku bi su a ƙasar da za ku shiga ku mallaki.
تمام قوانینی را که یهوه، خدایم به من داده است، به شما یاد داده‌ام. پس وقتی به سرزمین موعود وارد شده، آن را تسخیر نمودید از این قوانین اطاعت کنید.
6 Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al’ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa’ad da al’ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, “Ba shakka, wannan babbar al’umma tana da hikima da ganewa.”
اگر این دستورها را اجرا کنید به داشتن حکمت و بصیرت مشهور خواهید شد. زمانی که قومهای مجاور، این قوانین را بشنوند خواهند گفت: «این قوم بزرگ از چه حکمت و بصیرتی برخوردار است!»
7 Wace al’umma ce mai girma haka wadda allolinta take kusa da su yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu a duk sa’ad da muka yi addu’a gare shi?
هیچ قومی، هر قدر هم که بزرگ باشد، مثل ما خدایی مانند یهوه خدای ما ندارد که در بین آنها بوده، هر وقت او را بخوانند، فوری جواب دهد.
8 Wace al’umma ce mai girma haka wadda take da ƙa’idodi da dokoki masu adalci kamar waɗannan ƙunshin dokokin da nake sa a gabanku a yau?
هیچ قومی، هر قدر هم که بزرگ باشد، چنین احکام و قوانین عادلانه‌ای که امروز به شما یاد دادم، ندارد.
9 Ku kula, ku kuma lura da kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da idanunku suka gani, ko kuwa ku bari su fita daga zuciyarku muddin ranku. Ku koyar da su ga’ya’yanku, da’ya’yan’ya’yanku.
ولی مواظب باشید و دقت کنید مبادا در طول زندگی‌تان آنچه را که با چشمانتان دیده‌اید فراموش کنید. همهٔ این چیزها را به فرزندان و نوادگانتان تعلیم دهید.
10 Ku tuna da ranar da kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa’ad da ya ce mini, “Ka tara mutane a gabana, don su ji maganata, su koya yin mini bangirma muddin ransu a ƙasar, su kuma iya koyar da su ga’ya’yansu.”
به یاد آورید آن روزی را که در کوه حوریب در برابر خداوند ایستاده بودید و او به من گفت: «مردم را به حضور من بخوان و من به ایشان تعلیم خواهم داد تا یاد بگیرند همیشه مرا احترام کنند و دستورهای مرا به فرزندانشان بیاموزند.»
11 Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutse yayinda yana cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma baƙin gizagizai da kuma baƙin duhu.
شما در دامنهٔ کوه ایستاده بودید. ابرهای سیاه و تاریکی شدید اطراف کوه را فرا گرفته بود و شعله‌های آتش از آن به آسمان زبانه می‌کشید.
12 Sai Ubangiji ya yi magana daga wutar. Kuka ji furcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji.
آنگاه خداوند از میان آتش با شما سخن گفت. شما کلامش را می‌شنیدید، ولی او را نمی‌دیدید.
13 Ya furta alkawarinsa gare ku, Dokoki Goma, waɗanda ya umarce ku ku bi, ya kuma rubuta su a alluna biyu.
او قوانینی را که شما باید اطاعت کنید یعنی «ده فرمان» را اعلام فرمود و آنها را بر دو لوح سنگی نوشت.
14 Sa’an nan Ubangiji ya umarce ni a wannan lokaci, in koya muku ƙa’idodi da dokokin da za ku bi a ƙasar da kuke hayewa Urdun don mallake.
آری، در همان وقت بود که خداوند به من دستور داد قوانینی را که باید بعد از رسیدن به سرزمین موعود اجرا کنید به شما یاد دهم.
15 Ba ku ga wata siffa a ranar da Ubangiji ya yi magana da ku a Horeb daga wuta ba. Saboda haka ku lura da kanku sosai,
شما در آن روز در کوه حوریب وقتی که خداوند از میان آتش با شما سخن می‌گفت، شکل و صورتی از او ندیدید. پس مواظب باشید
16 don kada ku lalace, ku kuma yi wa kanku gunki, siffa ta wani kama, ko a kamannin namiji, ko kuwa ta mace,
مبادا با ساختن مجسمه‌ای از خدا خود را آلوده سازید، یعنی با ساختن بُتی به هر شکل، چه به صورت مرد یا زن،
17 ko a kamannin wata dabba a duniya, ko na wani tsuntsun da yake tashi a sama,
و چه به صورت حیوان یا پرنده،
18 ko kuwa a kamannin wata halittar da take rarrafe a ƙasa, ko na wani kifi a cikin ruwaye a ƙarƙashi.
خزنده یا ماهی.
19 Sa’ad da kuka ɗaga ido kuka kali sama, kuka ga rana da wata, da taurari, da dukan halittun sama, sai ku kula fa, kada ku jarrabtu, ku ce za ku yi musu sujada, ko ku bauta musu; abubuwan nan Ubangiji Allahnku ne ya rarraba wa dukan al’umman da suke ko’ina a ƙarƙashin sararin sama.
همچنین وقتی به آسمان نگاه می‌کنید و تمامی لشکر آسمان یعنی خورشید و ماه و ستارگان را که یهوه خدایتان برای تمام قومهای روی زمین آفریده است می‌بینید، آنها را پرستش نکنید.
20 Amma ku, Ubangiji ya ɗauke ku, ya fid da ku daga matuya mai narken ƙarfe, wato, daga Masar, domin ku zama jama’arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau.
خداوند شما را از مصر، از آن کورهٔ آتش، بیرون آورد تا قوم خاص او و میراث او باشید، چنانکه امروز هستید.
21 Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, ya kuma yi rantsuwa cewa ba zan haye Urdun, in shiga ƙasan nan mai kyau da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo ba.
ولی به خاطر شما نسبت به من خشمناک گردید و به تأکید اعلام فرمود که من به آن سوی رود اردن یعنی به سرزمین حاصلخیزی که یهوه خدایتان به شما به میراث داده است نخواهم رفت.
22 Zan mutu a wannan ƙasa; ba zan haye Urdun ba; amma kuna gab da ƙetarewa, ku mallaki wannan ƙasa mai kyau.
من اینجا در این سوی رودخانه خواهم مرد، ولی شما از رودخانه عبور خواهید کرد و آن زمین حاصلخیز را تصرف خواهید نمود.
23 Ku yi hankali kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku; kada fa ku yi wa kanku gunki a kamannin wani abin da Ubangiji Allahnku ya hana.
هوشیار باشید مبادا عهدی را که خداوند، خدایتان با شما بسته است بشکنید! اگر دست به ساختن هرگونه بُتی بزنید آن عهد را می‌شکنید، چون خداوند، خدایتان این کار را به کلی منع کرده است.
24 Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai ƙuna, Allah ne mai kishi.
زیرا یهوه خدای شما آتشی سوزاننده و خدایی غیور است.
25 Bayan kun haifi’ya’ya da jikoki, kuka kuma zauna na dogon lokaci a ƙasar, in har kuka lalace, kuka kuma yi wani irin gunki, kuna aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku, kuna kuma sa shi fushi.
حتی اگر سالها در سرزمین موعود ساکن بوده، در آنجا صاحب فرزندان و نوادگان شده باشید، ولی با ساختن بت خود را آلوده کرده با گناهانتان یهوه خدایتان را خشمگین سازید،
26 Yau, na kira sama da duniya, su zama shaidata a kanku. Idan kuka yi rashin biyayya, lalle za ku hallaka nan da nan daga ƙasar da kuke ƙetare Urdun ku gāda. Ba za ku daɗe a cikinta ba, amma za a kawar da ku ƙaƙaf.
زمین و آسمان را شاهد می‌آورم که در آن سرزمینی که با گذشتن از رود اردن آن را تصاحب خواهید کرد، نابود خواهید شد. عمرتان در آنجا کوتاه خواهد بود و به کلی نابود خواهید شد.
27 Ubangiji zai watsar da ku a cikin mutane, ɗan kaɗan ne kaɗai za su ragu a cikin al’umman da Ubangiji zai kai ku.
خداوند شما را در میان قومها پراکنده خواهد کرد و تعدادتان بسیار کم خواهد شد.
28 A can za ku bauta wa allolin da mutum ya yi, na itace da dutse da ba sa gani, ba sa ji, ba sa ci, ba kuma iya sansanawa.
در آنجا، بتهایی را که از چوب و سنگ ساخته شده‌اند پرستش خواهید کرد، بتهایی که نه می‌بینند، نه می‌شنوند، نه می‌بویند و نه می‌خورند.
29 Amma daga can in kuka nemi Ubangiji Allahnku, da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, za ku same shi.
ولی اگر شما دوباره شروع به طلبیدن خداوند، خدایتان کنید، زمانی او را خواهید یافت که با تمام دل و جانتان او را طلبیده باشید.
30 Sa’ad da kuke cikin wahala saboda waɗannan abubuwan da suka same ku nan gaba, to, sai ku juyo ga Ubangiji Allahnku, ku kuma yi masa biyayya.
وقتی در سختی باشید و تمام این حوادث برای شما رخ دهد، آنگاه سرانجام به خداوند، خدایتان روی آورده، آنچه را که او به شما بگوید اطاعت خواهید کرد.
31 Gama Ubangiji Allahnku, Allah ne mai jinƙai; ba zai yashe ku ko yă hallaka, ko kuma yă manta da alkawarin da ya yi da kakanninku, wanda ya tabbatar da su da rantsuwa ba.
یهوه، خدای شما رحیم است، پس او شما را ترک نکرده، نابود نخواهد نمود و عهدی را که با پدران شما بسته است فراموش نخواهد کرد.
32 Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
در تمامی تاریخ، از وقتی که خدا انسان را روی زمین آفرید، از یک گوشهٔ آسمان تا گوشهٔ دیگر جستجو کنید و ببینید آیا می‌توانید چیزی شبیه به این پیدا کنید که
33 Akwai waɗansu mutanen da suka taɓa jin muryar Allah yana magana daga wuta, kamar yadda kuka ji har suka rayu?
قومی صدای خدا را که از میان آتش با آنها سخن گفته است مثل شما شنیده و زنده مانده باشد!
34 Akwai wani allahn da ya taɓa yin ƙoƙari yă ɗauko wa kansa wata al’umma daga wata al’umma, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu masu banmamaki da al’ajabai, ta wurin yaƙi, ta wurin hannu mai iko, da kuma hannu mai ƙarfi, ko kuwa ta wurin ayyuka masu bangirma da na banmamaki, kamar dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi saboda ku a Masar, a kan idanunku?
و آیا تا به حال خدایی کوشیده است که با فرستادن بلاهای ترسناک و آیات و معجزات و جنگ، و با دست نیرومند و بازوی افراشته و اعمال عظیم و ترسناک، قومی را از بردگی قومی دیگر رها سازد؟ ولی یهوه خدایتان همۀ این کارها را در برابر چشمان شما در مصر برای شما انجام داد.
35 An nuna muku dukan waɗannan abubuwa saboda ku san cewa Ubangiji, shi ne Allah; ban da shi, babu wani.
خداوند این کارها را کرد تا شما بدانید که فقط او خداست و کسی دیگر مانند او وجود ندارد.
36 Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, don yă hore ku. A duniya ya nuna muku wutarsa mai girma, kuka kuma ji kalmominsa daga wuta.
او هنگامی که از آسمان به شما تعلیم می‌داد اجازه داد که شما صدایش را بشنوید؛ او گذاشت که شما ستون بزرگ آتشش را روی زمین ببینید. شما حتی کلامش را از میان آتش شنیدید.
37 Domin ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓi zuriyarsu a bayansu, ya fitar da ku daga Masar ta wurin kasancewarsa da kuma ƙarfinsa mai girma,
چون او پدران شما را دوست داشت و اراده نمود که فرزندانشان را برکت دهد، پس شخص شما را از مصر با نمایش عظیمی از قدرت خود بیرون آورد.
38 don yă fitar da ku a gaban al’ummai da suka fi ku girma da kuma ƙarfi, ya kawo ku cikin ƙasarsu, don yă ba ku ita ta zama gādonku, kamar yadda yake a yau.
او قومهای دیگر را که قویتر و بزرگتر از شما بودند پراکنده نمود و سرزمینشان را به طوری که امروز مشاهده می‌کنید، به شما بخشید.
39 Ku sani, ku kuma riƙe a zuciya a wannan rana, cewa Ubangiji shi ne Allah a sama da kuma a ƙasa. Babu wani kuma.
پس امروز به خاطر آرید و فراموش نکنید که خداوند، هم خدای آسمانها و هم خدای زمین است و هیچ خدایی غیر از او وجود ندارد!
40 Ku kiyaye ƙa’idodi da umarnai, waɗanda nake ba ku a yau, domin zaman lafiyarku da kuma na zuriyarku bayan ba ku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.
شما باید قوانینی را که امروز به شما می‌دهم اطاعت کنید تا خود و فرزندانتان کامیاب بوده، تا به ابد در سرزمینی که خداوند، خدایتان به شما می‌بخشد زندگی کنید.
41 Sa’an nan Musa ya keɓe birane uku gabas da Urdun,
آنگاه موسی سه شهر در شرق رود اردن تعیین کرد
42 waɗanda duk wanda ya yi kisankai, in ba da gangan ba ne ya kashe maƙwabcinsa, wanda babu ƙiyayya tsakaninsu a dā, zai iya gudu zuwa. Zai iya gudu zuwa cikin ɗaya daga waɗannan birane, yă tsira da ransa.
تا اگر کسی ناخواسته شخصی را بکشد بدون اینکه قبلاً با او دشمنی داشته باشد، برای فرار از خطر به آنجا پناه ببرد.
43 Biranen kuwa su ne, Bezer a dutsen hamada, don mutanen Ruben; Ramot Gileyad, don mutanen Gad; da kuma Golan a Bashan, don mutanen Manasse.
این شهرها عبارت بودند از: باصر واقع در اراضی مسطح بیابان برای قبیلهٔ رئوبین، راموت در جلعاد برای قبیلهٔ جاد، و جولان در باشان برای قبیلهٔ منسی.
44 Wannan ita ce dokar da Musa ya sa a gaban Isra’ilawa.
وقتی قوم اسرائیل از مصر خارج شده و در شرق رود اردن در کنار شهر بیت‌فغور اردو زده بودند، موسی قوانین خدا را به آنها داد. (این همان سرزمینی بود که قبلاً اموری‌ها در زمان سلطنت سیحون پادشاه که پایتختش حشبون بود در آنجا سکونت داشتند و موسی و بنی‌اسرائیل وی را با مردمش نابود کردند.
45 Waɗannan su ne farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Musa ya ba su, sa’ad da suka fito daga Masar.
46 Sa’ad da suke a kwari kusa da Bet-Feyor, gabas da Urdun, a ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, da Musa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi sa’ad da suka fito daga Masar.
47 Suka mallaki ƙasarsa da kuma ƙasar Og sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa, gabas da Urdun.
آنها بر سرزمین او و بر سرزمین عوج، پادشاه باشان که هر دو از پادشاهان اموری‌های شرق رود اردن بودند غلبه یافتند.
48 Wannan ƙasa ta tashi daga Arower a kewayen Kwarin Arnon zuwa Dutsen Siyon (wato, Hermon),
این سرزمین از عروعیر در کنار رود ارنون تا کوه سریون که همان حرمون باشد، امتداد می‌یافت
49 ya kuma haɗa da dukan Araba gabas da Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.
و شامل تمام منطقهٔ شرق رود اردن که از جنوب به دریای مرده و از شرق به دامنهٔ کوه پیسگاه منتهی می‌شد، بود.)

< Maimaitawar Shari’a 4 >